• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Gasar Adabi karo Na Uku Don Bunƙasa Ilimin ‘Ya’ya Mata A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Aka Gudanar Da Gasar Adabi karo Na Uku Don Bunƙasa Ilimin ‘Ya’ya Mata A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da gasar adabin ne don bunƙasa ilimin ‘ya’ya mata karo na uku mai taken ‘Fatima Dikko Raɗɗa girls child education summit and literacy contest’

Ita dai wannan gasa an samar da ita ce da nufin karfafa guiwar ‘ya’ya mata musamman abin da ya shafi karatunsu tun daga matakin firamare har zuwa jami’a ta yadda za su riƙa samun wakilci a fannonin rayuwa.

  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
  • Gwamna Dikko Ya Amince Da Bude Asusun Bai-daya A Jihar Katsina

A karo na uku na wannan gasa, an zakulo ɗalibai daga ɓangarori huɗu da suka haɗa da ƙanana da manyan makarantun sakandire da masu karatu a matakin digiri na daya da na biyu domin fafatawa a wannan gasa wanda kungiyar ‘read Right Multipurpose education society’ suka saba shiryawa.

Ɗaliban da suka fafata a cikin wannan gasa su kimanin ɗalibai 41 daga ƙaramar sakandire sai kuma ɗalibai 54 daga babbar sakandire, sai ɗalibai 19 masu karatun digiri da kuma mutum biyu masu karatun digiri na biyu.

Daga cikin mahimman batutuwa da aka tattauna a wannan gasar ta bana sun haɗa da batun samar da tsaftattaccen ruwan sha da irin rawar da mata ke takawa wajan samar da tsaftataccen ruwan sha da batun ciwon daji ‘cancer’ da dai sauransu

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Haka kuma kowanne rukuni an fitar da na ɗaya zuwa na uku, inda aka ba su kyaututtuka da kuɗaɗe domin ƙara masu ƙwarin guiwa musamman abin da ya shafi karatunsu.

Tun da farko shugaban kungiyar ‘Read Right Multipurpose education society’ Aliyu Nasir Ƙanƙara ya bayyana wasu ayyukan wannan kungiyar inda ya ce, an samu gagarumar nasara a cikin wannan shekarar ta 2023.

“Mun ƙaddamar da rabon littattafai a ƙaramar hukumar Musawa da Dabai a ƙaramar hukumar Danja, mun yi gangamin wayar da kai kan sha’anin shugabanci da kuma bayar da abinci a lokacin watan Ramadan da ya gabata”. Inji shi

Ya ƙara da cewa a shirinsu na a koma makaranta ”Back to School Campaign’ sun samu nasarar mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta 7,500, sannan sun yi taron wayar da kai dangane da matsalar rikice-rikecen cikin gida da sauran batutuwa da suka shafi al’umma.

Ita ma a nata jawabin kwamishiniyar ilimi a matakin farko, Hajiya Hadiza Yar’adua, ta yi bayanin cewa irin wannan gasa na nuna irin yadda aka nuna kulawa ga ilimin ‘ya ‘ya mata

Kwamishinan ta ce ko ba komi l, an sanar da wata sabuwar hanya ta karfafa guiwar ‘ya’ya mata wanda hakan ba zai sa a bar su a baya ba ta bangarori da dama.

“Yanzu muryoyin ‘ya ‘ya mata za su fara yin amo na gaskiya, musamman abubuwan da suka shafi ilimi na zamani da kuma na addini” inji ta.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Katsina, Hajiya Zainab Musa Musawa, ta nuna mahimmancin yin ilimin ga ‘ya’ya mata musamman a wannan lokaci da ake da ƙalubale kala-kala na rayuwa.

A jawabinta mai ɗakin gwamnan jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa, ta nuna farin cikinta kan yadda ɗalibai suka nuna ƙwazo da jajircewa a lokacin wannan gasa da ta gudana.

Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa ta ce, haƙiƙa sun zama abin alfahari ga al’ummar jihar Katsina ta yadda da irin haka ne za su canza alƙiblar ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jihar Katsina da arewacin Nijeriya.

An kammala wannan gasa ta adabi da bunkasa ilimi ‘ya’ya mata da aka yi kwanaki biyu ana gudanarwa tare da raba kyaututtuka ga waɗanda suka samu nasarar lashe gasar a Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdabiGasaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 132 Sun Rasu A Girgizar Kasar Yankin Nepal

Next Post

Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 hour ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

3 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

6 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

8 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

9 hours ago
Next Post
Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

LABARAI MASU NASABA

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.