ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Gasar Adabi karo Na Uku Don Bunƙasa Ilimin ‘Ya’ya Mata A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
gasa

An gudanar da gasar adabin ne don bunƙasa ilimin ‘ya’ya mata karo na uku mai taken ‘Fatima Dikko Raɗɗa girls child education summit and literacy contest’

Ita dai wannan gasa an samar da ita ce da nufin karfafa guiwar ‘ya’ya mata musamman abin da ya shafi karatunsu tun daga matakin firamare har zuwa jami’a ta yadda za su riƙa samun wakilci a fannonin rayuwa.

  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
  • Gwamna Dikko Ya Amince Da Bude Asusun Bai-daya A Jihar Katsina

A karo na uku na wannan gasa, an zakulo ɗalibai daga ɓangarori huɗu da suka haɗa da ƙanana da manyan makarantun sakandire da masu karatu a matakin digiri na daya da na biyu domin fafatawa a wannan gasa wanda kungiyar ‘read Right Multipurpose education society’ suka saba shiryawa.

ADVERTISEMENT

Ɗaliban da suka fafata a cikin wannan gasa su kimanin ɗalibai 41 daga ƙaramar sakandire sai kuma ɗalibai 54 daga babbar sakandire, sai ɗalibai 19 masu karatun digiri da kuma mutum biyu masu karatun digiri na biyu.

Daga cikin mahimman batutuwa da aka tattauna a wannan gasar ta bana sun haɗa da batun samar da tsaftattaccen ruwan sha da irin rawar da mata ke takawa wajan samar da tsaftataccen ruwan sha da batun ciwon daji ‘cancer’ da dai sauransu

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Haka kuma kowanne rukuni an fitar da na ɗaya zuwa na uku, inda aka ba su kyaututtuka da kuɗaɗe domin ƙara masu ƙwarin guiwa musamman abin da ya shafi karatunsu.

Tun da farko shugaban kungiyar ‘Read Right Multipurpose education society’ Aliyu Nasir Ƙanƙara ya bayyana wasu ayyukan wannan kungiyar inda ya ce, an samu gagarumar nasara a cikin wannan shekarar ta 2023.

“Mun ƙaddamar da rabon littattafai a ƙaramar hukumar Musawa da Dabai a ƙaramar hukumar Danja, mun yi gangamin wayar da kai kan sha’anin shugabanci da kuma bayar da abinci a lokacin watan Ramadan da ya gabata”. Inji shi

Ya ƙara da cewa a shirinsu na a koma makaranta ”Back to School Campaign’ sun samu nasarar mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta 7,500, sannan sun yi taron wayar da kai dangane da matsalar rikice-rikecen cikin gida da sauran batutuwa da suka shafi al’umma.

Ita ma a nata jawabin kwamishiniyar ilimi a matakin farko, Hajiya Hadiza Yar’adua, ta yi bayanin cewa irin wannan gasa na nuna irin yadda aka nuna kulawa ga ilimin ‘ya ‘ya mata

Kwamishinan ta ce ko ba komi l, an sanar da wata sabuwar hanya ta karfafa guiwar ‘ya’ya mata wanda hakan ba zai sa a bar su a baya ba ta bangarori da dama.

“Yanzu muryoyin ‘ya ‘ya mata za su fara yin amo na gaskiya, musamman abubuwan da suka shafi ilimi na zamani da kuma na addini” inji ta.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Katsina, Hajiya Zainab Musa Musawa, ta nuna mahimmancin yin ilimin ga ‘ya’ya mata musamman a wannan lokaci da ake da ƙalubale kala-kala na rayuwa.

A jawabinta mai ɗakin gwamnan jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa, ta nuna farin cikinta kan yadda ɗalibai suka nuna ƙwazo da jajircewa a lokacin wannan gasa da ta gudana.

Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa ta ce, haƙiƙa sun zama abin alfahari ga al’ummar jihar Katsina ta yadda da irin haka ne za su canza alƙiblar ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jihar Katsina da arewacin Nijeriya.

An kammala wannan gasa ta adabi da bunkasa ilimi ‘ya’ya mata da aka yi kwanaki biyu ana gudanarwa tare da raba kyaututtuka ga waɗanda suka samu nasarar lashe gasar a Katsina.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.