• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kafa Sabon Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Kasar Sin
0
Yadda Aka Kafa Sabon Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Xi Jinping, mai jagorancin kasar Sin a sabon tafarki

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da aka cimma tarihi mai cike da daukaka na shekaru dari, da shiga wani sabon zamani, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS) ta shiga wani muhimmin lokaci mai matukar ma’ana a tarihinta.

A safiyar ranar 23 ga watan Oktoban shekarar 2022, a babban dakin taron jama’a dake nan birnin Beijing, cikakken zama karo na farko na sabon kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20, ya zabi mambobi 24 na hukumar siyasa ta kwamitin koli karo na 20, inda aka zabi Xi Jinping, da Li Qiang, da Zhao Leji, da Wang Huning, da Cai Qi, da Ding Xuexiang da kuma Li Xi a matsayin zaunannun mambobin hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, kana aka sake zaben Xi Jinping a matsayin babban sakataren kwamitin. Aka kuma amince da mambobin sakatariyar kwamitin koli, sannan aka tabbatar da mambobin hukumar soja ta kwamitin kolin. Bugu da kari, aka amince da shugabannin hukumar ladabtarwa ta kwamitin koli karo na 20 da aka zaba a cikakken zama na farko.

  • Ya Kamata Amurka Ta Hada Gwiwa Da Sin Don Mayar Da Huldar Dake Tsakaninsu Kan Hanyar Da Ta Dace

A muhimmin lokacin da aka kama turbar sabon tafarki na gina kasa ta zamani mai bin tsarin gurguzu a dukkan fannoni, da kokarin cimma babban buri na biyu, wato zamanintar da kasar Sin zuwa kasa mai karfi dake bin tsarin gurguzu, yayin da Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ta cika shekaru 100 da kafuwa, daukacin jam’iyyar, da dukkanin al’ummun kasar nan, suna fatan zabar wata babbar kungiya mai hadin kai da karfi da za ta jagorance su, wajen daukar nauyin dake bisa wuyanta. A karkashin jagorancin babban sakatare Xi Jinping, za a ci gaba da karfafa nasarorin da aka cimma, da shawo kan matsaloli, da kuma tinkarar hadurra da sauye-sauye yadda ya kamata, ta yadda za a samu nasarar cimma burika a fannoni daban daban a sabon zamani da sabon tafarki.

“Jam’iyyarmu babbar jam’iyya ce mai mambobi sama da miliyan 96, wadda ke rike da mulki a wata babbar kasa mai yawan al’umma fiye da biliyan daya, don haka, muna da babban nauyi a wuyanmu, nauyin dake kanmu ba karami ba ne. Dole ne ta kafa hadaddiyar kungiyar jagoranci a siyasance, mai hadin kai, karfi da kuma aiki tukuru. Maganganun da babban sakatare Xi Jinping ya yi, suna da ma’ana da hangen nesa.”

Bisa cikakken shirin kwamitin kolin jam’iyyar tare da Xi Jinping a matsayin jagora, an gudanar da ayyukan tantancewa da zabar sabbin shugabannin kwamitin koli yadda ya kamata.
Tun daga farkon shekarar 2022, babban sakatare Xi Jinping ya saurari ra’ayoyin sauran mambobin zaunannen kwamitin hukumar siyasa ta kwamitin koli, kan yadda za a zabi ’yan takarar sabuwar hukumar da za ta shugabanci kwamitin kolin JKS.

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

kwaminis
•An zabi mambobi 24 na hukumar siyasa ta kwamitin koli karo na 20, a yayin cikakken zama

Dukkansu sun yarda a saurari shawarwari da ra’ayoyi na wasu manyan jami’ai da nagartattun mutane fuska da fuska game da sabbin ’yan takara na sabuwar hukumar siyasa, da na zaunannen kwamitin, da na sakatariyar kwamitin koli na JKS, da manyan jami’an majalisar gudanarwa, da mambobin hukumar soja na kwamitin kolin, da sabbin ’yan takarar majalisar wakilan jama’ar kasar Sin da na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin, da dai sauransu.

A farkon lokacin zafi na shekarar 2022 a Zhongnanhai, inda kwamitin kolin JKS da majalisar gudanarwar kasar ke aiki, da misalin karfe 7 na safe, wani babban jami’i mai mukamin gwamna ko minista ya zo nan da wuri don shirya wata tattaunawa mai mahimmanci. A kwanaki biyu da suka wuce, ya samu sanarwar zuwa birnin Beijing, kuma bayan da ya iso Zhongnanhai ya san abin da tattaunawar ta kunsa.

A dakin hutu, ya karanta abubuwan da aka tsara gudanarwa, ciki har da “Shirye-shiryen da suka shafi Tattaunawa da Bincike”, “Jerin sunayen shugabannin jam’iyyar da na gwamnatin kasar”, “Jerin sunayen jami’ai ’yan jam’iyyar masu mukamin gwamna ko minista”……

An fara tattaunawa a hukumance da misalin karfe 9 na safe. Shugabannin kwamitin tsakiya sun yi musabaha gaba da gaba da mahalarta taron, inda suka saurari ra’ayoyi da shawarwari kan zaben sabbin shugabannin kwamitin tsakiyar.

Wannan ya nuna yadda ake gudanar da tattaunawa da bincike a fili.
Tun daga watan Afrilun shekarar 2022, babban sakatare Xi Jinping wanda ya ke fama da aiki a kullum, ya kan kebe lokaci na musamman don tattaunawa da kuma neman ra’ayoyi daga mambobin hukumar siyasa ta kwamitin koli masu ci, da sakatarori na ofishin sakatariyar kwamitin kolin JKS, da mataimakin shugaban kasar, da mambobin hukumar soja ta kwamitin koli, da yawansu ya kai 30.

kwaminis
•Jam’iyyar JKS na jagorantar kasar don cimma babban burin farfado da al’ummar Sinawa

Bisa shirin zaunannen kwamitin hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, daga watan Afrilu zuwa Yuli na shekarar 2022, manyan shugabannin kwamitin koli da abin ya shafa, sun saurari ra’ayoyin manyan shugabanni ’yan jam’iyyar da na hukumomin mulkin kasa, da na majalisar ba da shawarwari kan harkokin siyasa ta kasar, da manyan jiga-jigan ’yan jam’iyyar wadanda suke rike da mukaman gwamna ko minista, da manyan hafsoshin rundunonin soja, ciki har da kwamandoji da kwamishinoni na siyasa da dai sauransu, da kuma mambobin kwamitin koli na JKS karo na 19, wadanda yawansu ya kai 283. A nasu bangaren kuma, shugabannin hukumar soja ta kwamitin kolin JKS sun saurari ra’ayoyin kwamandojin soja da takwarorinsu manyan hafsoshi, da yawansu ya kai 35 game da sabbin mambobin hukumar soja ta kwamitin kolin jam’iyyar.

Sannu a hankali za a zabi manyan shugabannin ta hanyar bincike da nazari da tattaunawa, da sauraron ra’ayoyi, sake tattaunawa da yanke shawara yayin taruka don tsaida kuduri da ma sauran matakai. Dukkan matakan yin zaben, sun nuna kyautatuwar tsarin jam’iyya da na gwamnati na zaben shugabanni, da imani da hangen nesa da jam’iyyar ke da shi.

Bisa ra’ayoyi da shawarwari daga sassa daban-daban, babban sakatare Xi Jinping ya yi musayar ra’ayoyi da shawarwari a kai a kai da sauran mambobin zaunannen kwamitin hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS kan manufofi da tsare-tsare na kafa sabuwar hukumar shugabancin sabon kwamitin kolin. Bayan tsara kwarya-kwaryar shirin, babban sakatare Xi Jinping ya sake sauraron ra’ayoyin mambobin zaunannen kwamitin hukumar siyasa, da mambobin hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, da sakatarorin sakatariyar kwamitin kolin JKS. A kan haka ne aka gabatar da shirin sabbin mambobin shugabannin kwamitin kolin JKS.

Hukumar ladabtarwa da hukumar kula da harkokin jami’ai na kwamitin kolin JKS ne suka gabatar da shirin ’yan takara mambobin sabuwar hukumar ladabtarwa ga kwamitin kolin jam’iyyar JKS ta hanyar neman ra’ayoyi daga bangarori daban daban. Sannan, hukumar soja ta kwamitin kolin JKS ce ta shirya tarukan tattaunawa ta tabbatar da takardar dake kunshe da ’yan takarar mambobin sabuwar hukumar soja da za a kafa, sannan ta gabatar da wannan takarda ga kwamitin kolin JKS domin neman amincewa.

A ranar 28 ga watan Satumban shekarar 2022, zaunannen kwamitin hukumar ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya kira taro, don tattauna jerin sunayen sabbin mambobin hukumomin shugabanci na sabon kwamitin kolin JKS. A ranar 29 ga watan Satumba, an zartas da kuma amincewa da su a yayin taron hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS.

kwaminis
Xinhuamen, kofa ce ta Zhongnanhai, inda kwamitin kolin JKS da majalisar gudanarwar

A ranar 22 ga watan Oktoba, wadannan sabbin mambobin sabon kwamitin kolin JKS da na kwamitin ladabtarwa dake karkashin jagorancin kwamitin kolin JKS da aka zaba, sun samu amincewar wakilan da suka halarci babban taron wakilan jam’iyyar karo na 20.

Sannan a ranar 23 ga watan Oktoba, an zabi da kuma amincewa da sabbin mambobin hukumar siyasa da mambobin zaunannen kwamitin hukumar siyasa a yayin cikakken zama karo na farko na kwamitin kolin JKS karo na 20.

Mambobin sabbin hukumomin shugabancin kwamitin kolin JKS dukkansu suna da kwarewa wajen ciyar da aikin zamanantar da kasar Sin gaba, kuma suna da jajircewa wajen sauke nauyin dake wuyansu. Bugu da kari, sun samu amincewa sosai daga wajen jami’ai a matakai daban daban da jama’a fararen hula.

Da karfe 12 na ranar 23 ga Oktoba na shekarar 2022, a babban dakin taron jama’a, Xi Jinping, wanda aka sake zaben sa a matsayin babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, da sauran mambobin sabon zaunannen kwamitin hukumar siyasa ta kwamitin kolin, sun gana da ‘yan jaridun kasar Sin da na ketare wadanda suka ba da rahotannin babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20.

kwaminis
•Xi Jinping, wanda aka sake zaben sa a matsayin babban sakatare, da sauran mambobin sabon
zaunannen kwamitin hukumar siyasa ta kwamitin kolin, sun gana da ‘yan jaridun Sin da na
ketare

Daga bisani, babban sakatare Xi Jinping ya kewaya zauren taron, a madadin sabbin shugabanin kwamitin kolin jam’iyyar, inda ya yi nuni da cewa, yayin da aka doshi sabon tafarki, dole ne a ko da yaushe a ci gaba da sanya jama’a a gaban kome, da kuma dogaro da jama’a. Kuma dole ne a yi aiki tukuru, da sa kaimi ga juyin-juya-hali kan jam’iyyar, da yada dabi’un gama gari na daukacin bil-Adama.

Wannan shi ne imanin da jagoran kasar ke da shi a sabon zamani, da nauyin da ke bisa wuyansa a sabon tafarki, da yadda zai jagoranci jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wadda aka kafa ta yau shekaru sama da 100 da suka gabata wajen kara samun nasara, da farfadowar al’ummun kasar baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Hada Gwiwa Da Sin Don Mayar Da Huldar Dake Tsakaninsu Kan Hanyar Da Ta Dace

Next Post

Bagudu Ya Amince Da Nadin Sarakunan Gargajiya 2 A Masarautar Yauri Ta Jihar Kebbi

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

3 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

10 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

10 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

11 months ago
Zambiya
Daga Kasar Sin

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

1 year ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Next Post
Bagudu Ya Amince Da Nadin Sarakunan Gargajiya 2 A Masarautar Yauri Ta Jihar Kebbi

Bagudu Ya Amince Da Nadin Sarakunan Gargajiya 2 A Masarautar Yauri Ta Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.