• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

by yahuzajere
2 years ago
ACG James Sunday

Gwambawa a karkashin Kungiyar Tsofaffin Daliban Makarantar Sakandaren Kimiyya ‘yan ajin 1984 da kuma Kungiyar ‘Yan Ajin Digiri na Biyu a Fannin Nazarin Harkokin Kasashen Waje da Difilomasiyya (MIAD) da suka kamala a 2008, sun shirya wa ACG James Sunday kwarya-kwaryan bikin taya murnar samun karin girman a Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS).

James Sunday ya samu Karin girma daga Kwanturola na Jiha zuwa mukamin Mataimakin Kwanturola Janar (ACG)

An gudanar da kwarya-kwaryar taron bikin ne a harabar makarantar sakandaren ta kimiyya da ke Gombe a farkon makon nan.

Daruruwan mutane da ‘yan’uwa da abokan arziki da suka halarta, sun yi ta fatan alheri ga babban jami’in tare da addu’ar samun nasara a sabon mukamin nasa.

Da yake Karin bayani ga wakilinmu, ACG James Sunday ya yi godiya ga wadanda suka shirya bikin wanda ya ce saboda kauna ce tsantsa suka yi masa haka, kana ya gode wa Kwanturola Janar ta NIS, CGI Caroline Wura-Ola Adepoju da Ministan Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa tabbatar musu da Karin girma kana ya nanata kudirinsa na ci gaba da aiki tukuru domin sauke nauyin da tsarin mulkin kasa ya dora musu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

  • Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina
  • Tinubu Ga Gwamnoni: Dole Ne Mu Tabbatar Da Zaman Lafiya A Nijeriya

 

ACG James Sunday wanda ya kammala makarantar sakandaren ta Gombe kuma daga bisani ya halarci Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Gombe inda ya kammala tare da samun lambar yabo a matsayin dalibi mafi kwazo a shekarar 1987, har ila yau ya halarci Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna tare da nazartar Ilimin Fasahar Masana’antu.

Ya fara aiki da Hukumar Shige da AFice ta Kasa a 1989 inda ya halarci makarantar horaswa ta jami’an hukumar da ke Kano tare da kammalawa da samun lambobin yabo da suka hada ta minista da kuma ta darakta wanda ake bai wa jami’I mafi kwazo.

Shi ne ya zama jami’in hulda da jama’a na farko (PRO) a NIS da ya fara rike matsayin daga matakin babban ofishin jiha a Jihar Ribas, sai kuma ya zama na ofishin babbar shiyya ta Zone B mai shalkwata a Kaduna daga bisani kuma ya zama Babban Jami’in Hulda da Jama’ar ta NIS baki daya a shalkwatarta da ke Abuja

Shi ne ya fara zama jami’in sashen aikin hadin gwiwa a tsakanin Rundunar ‘Yansandan Duniya da NIS wanda sashen ne ya samar da hanyoyin da hukumomin biyu suka kafa sashen sadarwa a shalkwatar ‘yansanda ta kasa daga bisani aka yi nasarar kaddamar da manhajar rundunar ‘yansandan duniya da ke aiki dare da rana kullum. Wannan ya taimaka gaya wajen hadin gwiwar aiki a tsakanin Nijeriya da ‘yansandan duniya musamman a tsakanin hukumomin tsaro da NIS ke jagorantarsu a wannan fannin.

Bugu da kari, ACG James Sunday, ya zama jami’i na farko da aka nada mai bai wa ministan cikin gida shawara a kan harkar tsaro a lokacin da ake tsananin bukatar basirar wani kwararre ta fuskar tattara bayanan sirri domin magance fashe-fashen gidajen yari da kuma yin gyaran fuska ga ayyukan gidajen yari. Ya yi wannan aikin ne a matsayin jami’in da aka ba da aron sa.

Yanzu haka, ACG James Sunday, shi ne babban jami’i shalkwatar NIS ta shiyyar Zone C mai kula da arewa maso gabas da ta kunshi Jihohin Adamawa, Bauhci, Borno, Gombe, Filato da kuma Yobe,

ACG James Sunday jami’i ne da ya yi shuhura a fannin aikin yada labarai da sadarwa wanda ake matukar girmamawa a gamayyar hukumomin tsaro ta FOSSRA da ta kunshi daukacin jami’an hulda da jama’a. Har ila yau, marubuci ne da ya wallafa littafai, da Makalu, kana yana da sha’awar wasan kwallon dawaki da na golf, sannan mutum ne mai son Ubangiji, magidanci da yake da aure da kuma ‘ya`ya masu albarka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe
Labarai

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Next Post
Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.