• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwambawa a karkashin Kungiyar Tsofaffin Daliban Makarantar Sakandaren Kimiyya ‘yan ajin 1984 da kuma Kungiyar ‘Yan Ajin Digiri na Biyu a Fannin Nazarin Harkokin Kasashen Waje da Difilomasiyya (MIAD) da suka kamala a 2008, sun shirya wa ACG James Sunday kwarya-kwaryan bikin taya murnar samun karin girman a Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS).

James Sunday ya samu Karin girma daga Kwanturola na Jiha zuwa mukamin Mataimakin Kwanturola Janar (ACG)

An gudanar da kwarya-kwaryar taron bikin ne a harabar makarantar sakandaren ta kimiyya da ke Gombe a farkon makon nan.

Daruruwan mutane da ‘yan’uwa da abokan arziki da suka halarta, sun yi ta fatan alheri ga babban jami’in tare da addu’ar samun nasara a sabon mukamin nasa.

Da yake Karin bayani ga wakilinmu, ACG James Sunday ya yi godiya ga wadanda suka shirya bikin wanda ya ce saboda kauna ce tsantsa suka yi masa haka, kana ya gode wa Kwanturola Janar ta NIS, CGI Caroline Wura-Ola Adepoju da Ministan Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa tabbatar musu da Karin girma kana ya nanata kudirinsa na ci gaba da aiki tukuru domin sauke nauyin da tsarin mulkin kasa ya dora musu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

  • Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina
  • Tinubu Ga Gwamnoni: Dole Ne Mu Tabbatar Da Zaman Lafiya A Nijeriya

 

ACG James Sunday wanda ya kammala makarantar sakandaren ta Gombe kuma daga bisani ya halarci Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Gombe inda ya kammala tare da samun lambar yabo a matsayin dalibi mafi kwazo a shekarar 1987, har ila yau ya halarci Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna tare da nazartar Ilimin Fasahar Masana’antu.

Ya fara aiki da Hukumar Shige da AFice ta Kasa a 1989 inda ya halarci makarantar horaswa ta jami’an hukumar da ke Kano tare da kammalawa da samun lambobin yabo da suka hada ta minista da kuma ta darakta wanda ake bai wa jami’I mafi kwazo.

Shi ne ya zama jami’in hulda da jama’a na farko (PRO) a NIS da ya fara rike matsayin daga matakin babban ofishin jiha a Jihar Ribas, sai kuma ya zama na ofishin babbar shiyya ta Zone B mai shalkwata a Kaduna daga bisani kuma ya zama Babban Jami’in Hulda da Jama’ar ta NIS baki daya a shalkwatarta da ke Abuja

Shi ne ya fara zama jami’in sashen aikin hadin gwiwa a tsakanin Rundunar ‘Yansandan Duniya da NIS wanda sashen ne ya samar da hanyoyin da hukumomin biyu suka kafa sashen sadarwa a shalkwatar ‘yansanda ta kasa daga bisani aka yi nasarar kaddamar da manhajar rundunar ‘yansandan duniya da ke aiki dare da rana kullum. Wannan ya taimaka gaya wajen hadin gwiwar aiki a tsakanin Nijeriya da ‘yansandan duniya musamman a tsakanin hukumomin tsaro da NIS ke jagorantarsu a wannan fannin.

Bugu da kari, ACG James Sunday, ya zama jami’i na farko da aka nada mai bai wa ministan cikin gida shawara a kan harkar tsaro a lokacin da ake tsananin bukatar basirar wani kwararre ta fuskar tattara bayanan sirri domin magance fashe-fashen gidajen yari da kuma yin gyaran fuska ga ayyukan gidajen yari. Ya yi wannan aikin ne a matsayin jami’in da aka ba da aron sa.

Yanzu haka, ACG James Sunday, shi ne babban jami’i shalkwatar NIS ta shiyyar Zone C mai kula da arewa maso gabas da ta kunshi Jihohin Adamawa, Bauhci, Borno, Gombe, Filato da kuma Yobe,

ACG James Sunday jami’i ne da ya yi shuhura a fannin aikin yada labarai da sadarwa wanda ake matukar girmamawa a gamayyar hukumomin tsaro ta FOSSRA da ta kunshi daukacin jami’an hulda da jama’a. Har ila yau, marubuci ne da ya wallafa littafai, da Makalu, kana yana da sha’awar wasan kwallon dawaki da na golf, sannan mutum ne mai son Ubangiji, magidanci da yake da aure da kuma ‘ya`ya masu albarka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaACGArewa Maso GabasHukumar Shige Da FiceImmigrationNISNorth EastSecurity
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina

Next Post

Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da É—umi-É—uminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

12 minutes ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

12 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

13 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

14 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

15 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

16 hours ago
Next Post
Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

Ta Shiga Caji Ofis Ta Harbe Saurayinta Dan Sanda Har Lahira 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.