• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Taro Kan Alfanun Manufar Gyare-gyaren Sin A Sabon Zamani A Abuja

by Sani Anwar
1 year ago
Taro

A ranar Alhamis 25 ga Yuli, 2024, aka gudanar da wani taron kara wa juna sani a Cibiyar Al’adun Kasar Sin da ke Babban Birnin Tarayya Abuja mai taken “Gyare-gyaren kasar Sin a Sabon Zamani”.

Taron wanda aka gudanar bisa hadin gwiwar cibiyar al’adun da Hukumar Kafofin Watsa Labarai ta Kasar Sin (CMG) ta samu halartar kwararru da manyan baki wadanda suka yi karin haske a kan gyare-gyaren da kasar Sin ta tsunduma yi da kuma alfanunsu ga al’ummar duniya.

  • Majalisar Dattawa Ta Bukaci NEMA Ta Kai Wa Manoman Citta Dauki A Kaduna
  • Sin Ta Damu Kisan Shugaban Hamas Zai Iya Haifar Da Babban Tashin Hankali A Gabas Ta Tsakiya

An fara taron ne da gabatar da jawabin Mataimakin Daraktan Sashen Yada Labarai na Kwamitin Tsakiya na Jam’iyyar CPC kuma Darakta Janar na Hukumar Kafofin Watsa Labarai ta Kasar Sin, Mista Shen, inda ya nuna muhimmancin dorewar hadin gwiwa tare da mika godiya ga mahalarta taron.

Mista Shen, ya jaddada wajibcin hadin kai a tsakanin al’ummomin duniya domin cimma muradun ci gaba da kowa da kowa ke hankoron gani.

Har ila yau, masu gabatar da jawabai daban-daban a wurin taron sun yi gamsassun bayanai game da rawar da kasar Sin ke takawa wajen taimaka wa ci gaban kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Musamman wacce ta yi fashin baki a kan tasirin da kasar Sin ke yi wajen bunkasa tattalin arzikin duniya, Fa’iza Muhammed, ta ce ba karamar gudunmawa kasar Sin ta bayar wajen daidaita turbar habakar tattalin arzikin Nijeriya ba.

A nata bangaren, wakiliyar Ministar Bunkasa Yawon Bude, Misis Patricia Naria, ta mayar da hankali ne a kan yadda za a ciyar da harkokin yawon bude ido gaba a Nijeriya, kana ta nemi a karfafa matasa domin takaita kwararar mutane daga kauyuka zuwa birane.

Shi kuwa, Mista Raphael Oni, ya yi bayani ne a kan abubuwan da za a iya cimmawa idan aka samu hadin gwiwa da inganta kwazon aiki tsakanin kasashen duniya, kana ya yi tsokaci a kan irin rawar da Sin ke takawa wajen samar da ma’aikata a sassa daban-daban na ci gaban Nijeriya.

Shugaban Kungiyar ‘Yan Nijeriya Da Suka Samu Horo a Kasar Sin, Malam Mohammed Sulaiman, ya yi karin haske a kan muradun ci gaban kasa da Sin ta sanya a gaba da kuma kokarin da take yi na zamanantar da harkokinta tare da tabbatar da dorewar bunkasar duniya da zurfafa ci gaban kimiyya.

Ya kuma bayyana cewa, ga masu lura da matakin ci gaban kasar Sin, za su fahimci yadda kasar ta dage wajen fafutukar ganin su ne kan gaba a tsakanin sauran kasashen duniya, a bangaren tattalin arzikin kasa, domin samar da wadata a yankunansu.

Zauran majalisa ta uku, ya bai wa China damammaki iri daban-daban, wadanda suka hada da kamfanoni mallakar gwamnati da kuma sha’awar fuskantar babban kalubale na dunkulewar duniya wuri daya, in ji shi.

Sulaiman ya ci gaba da cewa, taron bana kan sauye-sauyen tattalin arziki da zamantakewa a kasar Sin, mai yiwuwa nan da shekarar 2029 a sake nazari a kan sabbin kalubalen da ke tunkarar duniya baki-daya.

Haka zalika, kasar Sin ta mayar da hankali wajen kyautata masana’antu gwamnati a matsayin na sahun gaba tare kuma da kyautata harkin bin doka da oda a fadin kasar baki-daya.

Daga bangaren Mista Okon Emmanuel kuwa, ya nuna muhimmancin shigar da matasa ne cikin harkokin yawon bude ido domin a dama da su, yayin da ita kuma Edi-ima Ekpety ta yi bayyana abubuwa masu ban sha’awa da ta koya a kasar Sin lokacin da take karatu a can inda ta nuna alfanun sanin al’adun juna da kuma damammakin karo ilimi da ake samu.

Ekpety Edi-ima; ta bayyana abubuwan da ta koya da kuma irin abubuwan da ci karo da su na ban sha’awa a fadin kasar.

Edi-ima ta ce, ta ziyarci kasa Sin ne kwanan nan; domin halartar taron taron kara wa juna sani, wanda ya kunshi mutum 18 daga kasashe bakwai na yankin kudu maso kudu.

Haka zalika, an shirya taron kara wa juna sanin ne; don sake karfafa alakar kasar Sin da kuma kasashen nahiyar kudu maso kudu da ke yankin Afirka. Babu shakka, wannan ziraya a cewarta, ta ba damar sanin wani bangare na rayuwar Sinawa da kuma irin ci gaban da suka samu.

Ta kara dacewa, abu na farko da ya fara burg eta shi ne, ganin yadda aka shuka filawa a kan hanyoyinsu, wanda ya sake kawata kasar yadda ya kamata. “Duk titinan da ka bi, haka za ka samu wadannan filawowi masu matukar ban sha’awa da kuma burgewa,” in ji ta.

Hakanan, a bangaren abin da ya shafi harkokin sufuri, mun koyi yadda za mu yi amfani da jirgin kasa da hawa motoci.

An dai kammala taron ne da jawabin mai gabatar da taron wanda ya nuna muhimmancin abubuwan da baki masu gabatar da jawabai suka bayyana tare da daukar hotuna da ke nuna sabunta hadin kai da zumunci a tsakanin mahalarta taron.

Za a iya cewa taron na kara wa juna sani da aka gabatar, ya samar da wata kafa ta tattaunawa da musanyar ra’ayoyi da kuma Karin haske a kan manufar gyare-gyaren da Sin ke yi da yadda abin zai amfanar da duniya tare da jaddada muhimmancin hadin gwiwa a tsakanin Nijeriya da Sin domin a gudu tare a tsira tare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Wakilin CMG Ya Zanta Da Shugaban Kasar Timor-Leste

Wakilin CMG Ya Zanta Da Shugaban Kasar Timor-Leste

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.