• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Wa Kwanturola Janar Na NIS Ado Da Sabon Muƙaminsa

Mun Yi Dace Da Samun Isah Jere A NIS – Aregbesola

by yahuzajere
3 years ago
in Rahotonni
0
NIS

Lokacin da ake nada wa mukaddashin Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Idris Jere sabon mukaminsa

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Ogbeni Aregbesola ya bayyana cewa ba ƙaramin dace aka yi ba da aka samu Isah Idris Jere a matsayin muƙaddashin Kwanturola Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS).

Ya bayyana haka ne a ranar Laraba jim kaɗan bayan ya yi wa muƙaddashin Kwanturola Janar ɗin ado da sabon muƙaminsa a ɗakin taro na Hukumar Gudanarwar Rundunonin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB), da ke Unguwar Area 1 a Abuja.

 

Lokacin makala saka masa sabuwar hular mukaminsa na Kwanturola Janar
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Ganduje Ya Ciyo Bashin Biliyan 10 Don Sayen Na’urar CCTV

Aregbesola wanda ya maƙala muƙamin tare da taimakon wani na hannun daman Isah Idris Jere, Alhaji Ibrahim Usman Yakasai, ya bayyana cewa suna da tabbacin zaɓin da Shugaba Buhari ya yi masa a matsayin wanda zai jagoranci hukumar ta NIS, zai amfanar da ƙasa da ‘yan ƙasa bisa la’akari da ƙwazonsa na aiki.

“Tabbas Isah Jere ya cancanci wannan matsayi, mutum ne mai ƙwazo. Godiya ga Shugaba Buhari da ya amince a naɗa shi a matsayin muƙaddashin CGI, daga yanzu kar wani ya ƙara ce masa DCG, ya zama cikakken Kwanturola Janar, duk da cewa za a riƙa kiran sa a matsayin muƙaddashi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

“Jere yana magana da harsuna daban-daban, idan yana magana da yarabanci sai na ji mamaki. Haka harshen Ibo ba za ka ce ba harshensa na gado ba ne. Na kasa haƙuri, wata rana na tambaye shi, Jere ina ka koyi waɗannan harsunan, sai ya ce mun ya yi mu’amala da aiki a wurare mabanbanta na ƙasar nan. Shi ya sa nake ganin harsunan da ba ya ji na ƙabilun ƙasar nan kaɗan ne kawai.

“Haƙiƙa mun samu shugaba mai son aiki, mai ƙwazo, wannan abu lada ne da Allah ya ba ka a madadin ƙwazon da kake nunawa. Ina taya ka murna tare da iyalai da ‘yan’uwanka a kan wannan muƙami.” In ji shi.

NIS
Lokacin da ake karanta tarihinsa kafin a kai ga daura masa sabon mukamin

Ministan ya kuma yi tsokaci a kan tsaikon da ake samu na Biza da Fasfo, inda ya ce, “Babu inda ba a samun ƙarancin fasfo a duk duniya. Na faɗa na kuma ƙara faɗa. Amma yanzu bisa abubuwan da aka sa a gaba, za a shawo kan komai. Kullum ina karanta ƙorafe-ƙorafen mutane a social media, amma nakan tambayi kaina, wai ma mene ne wanan? Sai na tuna cewa duk duniya ta na’ura ake neman fasfo. Dole sai an bi na’ura, don haka muka kawo tsarin da kowa zai iya nema a duk inda yake, daga nan za a ba shi lokacin da zai zo ya amsa. Kodayake ya danganta da yawan tururuwar jama’a a yankin da mutum yake nema. Misali, a Ikoyi, tururuwan jama’a da ake samu a can ya kai kusan kashi 50 na yawan tururuwar da ake samu a dukkan ofisoshin fasfo.

“Ina roƙon ‘Yan Nijeriya su ba mu goyon baya, su fallasa masu badaƙala a bayan fage. Mun yi alƙawarin cewa za mu ɗauki mataki na ba-sani-ba-sabo. Kuma yana da kyau mutane su fahimci cewa, bubuwan da ake yaɗawa galibinsu zuƙi ta malle ne. Kai, in da ma akwai wani abu da ya fi gaban a kira shi da ƙarya to shi suke yi.” Ya bayyana.

  • Sojoji Sun Tsinci Daya Daga Cikin Matan Chibok Da Boko Haram Suka Sace

Tun da farko sai da, ɗaya daga cikin Kwamishina a Hukumar Gudanarwar, Mista Bassey ya gabatar da muƙaddashin CGI Isah Idris Jere a gaban ministan da sauran waɗanda suka halarci ƙwarya-ƙwaryan bikin, kafin a fara duk abubuwan da suka wakana.

Da take gabatar da taƙaitaccen tarihinsa, Sakatariyar Hukumar Gudanarwar, Hajiya Aisha, ta bayyana cewa an haife shi ne a garin Jere da ke Ƙaramar Hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna a ranar 30 ga Disambar 1962. Ya yi karatunsa na Firamare a Makarantar LEA Jere, sannan ya tafi Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Katsina, kana daga bisani ya halarci Jami’ar Bayero da ke Kano inda ya yi digiri a fannin aikin jarida. Ya fara aiki da Hukumar Raya Birnin Tarayya Abuja daga bisani ya sauya ya koma Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa.

Ita ma da take tsokaci a kansa, Wakiliyar Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Cikin Gida, Misis Morimi, ta yaba da kyawawan halayensa, tana mai cewa “a kowane lokaci idan aka kira shi yana amsawa, duk lokacin da aka ce masa ga wata matsala ta taso nan da nan zai yi tsayin daka wajen magancewa. Mutum ne da ya yarda da kansa, yakan zo shi kaɗai cikin kayan gida, ba shi da tsoro game da tsaron kansa. A gaskiya mun ga sabuwar fuska a wannan matsayi da za ta zama mai albarka ga NIS,” in ji ta.

Da yake mayar da jawabi bayan ɗaura masa muƙamin, Muƙaddashin Kwanturola Janar Isah Idris Jere, ya yi godiya ga Allah Ta’ala da ya sahale masa wannan matsayin. Kana ya gode wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da Minista Aregbesola da dukkan shugabannin gudanarwar hukumar waɗanda suka ba shi goyon baya tun daga lokacin da ya karɓi ragamar riƙon hukumar a bara.

Ya ƙara da cewa, “Burina shi ne na mayar da hankali wajen bunƙasa NIS ta iya gasa da kowacce irin ta a duniya. Manyan abubuwan da na fi mayar da hankali a kai su ne batun inganta tsaron iyakokin ƙasa ta hanyar amfani da na’urorin aiki na zamani, da ƙara inganta harkokin fasfo domin ɗorawa a kan nasarorin da aka samu da rage yawan cunkoso da kuma tabbatar da walwalar jami’ai.

NIS

Manya da ƙananan mataimakan muƙaddashin Kwanturola Janar Isah Idris Jere suka rufa masa baya zuwa Hukumar Gudanarwar Rundunonin na Ma’aikatar Cikin Gida domin ɗaura masa muƙamin nasa.

Idan ba a manta bad ai, a makon da ya gabata, CGI Isah Idris Jere ya yi wa manyan jami’ai 94 da suka samu ƙarin girma ado da sababbin muƙamansu a shalkwatar hukumar da ke Abuja, yayin da ragowar huɗun aka yi musu a Ma’aikatar Cikin Gida.

Jimillar sabbin waɗanda aka ƙara wa girma zuwa muƙamin ƙananan mataimakan Kwanturola Janar sun kai 24 da Kwanturololi 70 waɗanda duka aka yi musu ado da sabbin muƙaman nasu a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da ya samu halartar takwarorin NIS da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Cikin Gida da sauran manyan jagororin Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB.

Daga cikin manyan jami’an da aka saka musu sabbin muƙaman nasu akwai DCG Oluremi Talabi, DCG Josephine Kwazu, DCG Modupe Anyalechi da kuma DCG Muhammad Aminu Muhammad.

Daga cikin ƙananan mataimakan Kwanturola Janar na NIS din kuma akwai ACG Kemi Nandap, babbar jami’ar da ke kula da shige da fice a Filin Jiragen Sama na Murtala Muhammad da ke Legas, da babban jami’in harkokin ofishin CGI da aka sauya kwanan nan, ACG Ahmad Bauchi Aliyu da kuma Kwanturola Mustapha Ahmad, mataimaki na musamman ga CGI a fannin gudanar da ayyuka.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Kyakkyawan Tagomashi A Watan Mayu

Next Post

‘Yan Nijeriya Za Su Fara More Karin Hasken Wutar Lantarki Da Aka Samu Daga 1 Ga Yuli – NERC

Related

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

1 hour ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

3 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

3 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

4 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

4 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

1 month ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Za Su Fara More Karin Hasken Wutar Lantarki Da Aka Samu Daga 1 Ga Yuli – NERC

‘Yan Nijeriya Za Su Fara More Karin Hasken Wutar Lantarki Da Aka Samu Daga 1 Ga Yuli – NERC

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.