• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi

by Dausayin Musulunci
2 months ago
in Addini
0
Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zakatul Fidir, ma’ana Zakkar Shan Ruwa ita ce da Hausa wasu ke ce mata Zakkar Fidda Kai. Zakkar wajibi ce a kan kowane Musulmi, yaro ko babba, namiji ko mace, da ko bawa. Ta wajaba a kan mutum da wadanda suke karkashinsa, wato wadanda ciyar da su yake kansa. Matansa da ‘ya’yansa da masu yi masa hidima wadanda yake rike da su yake ciyar da su.

Bayar da zakkar ta zama wajibi ga duk Musulmin da ya mallaki abincin da zai ci shi da iyalansa na kwana da yini kuma koda mudu daya na hatsi ya ragu masa. Abin da ake nufi shi ne, idan mutum yana da abincin da zai ishe shi ci tare da iyalansa, bayan ya ware wannan sai ya kasance an samu ragowar mudu daya, Zakkar ta hau kansa. Amma wanda ba shi da shi ta fadi a kansa, sai dai idan ya samu ya bayar, ta zama kamar bashi kenan.

  • Abin Da Masu Hannu Da Shuni Ya Kamata Su Rika Yi A Kan Rabon Zakkah
  • Bayani A Kan Zakkar Shan Ruwa Da Sallar Idi

Amfanin Bayar Da Zakkar

Amfanin bayar da Zakkar shi ne domin mutum ya tsarkake kansa daga suratai marasa amfani ko batsar da ya aikata a cikin watan Azumin Ramadan domin ibadar da ya yi ta Azumi ta kuvuta lafiya kalau. Haka nan amfaninta ya hada da ciyar da talakawa da almajirai wadanda ba su da abincin da za su ci don yaye masu kunci na rashin abincin, domin kuma kar a gan su sun fito suna bara.

An farlanta Zakkar ta Shan Ruwa ce a watan Sha’aban, bayan Hijirar Annabi (SAW) da shekara biyu.

Labarai Masu Nasaba

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

Yadda Ake Ba Da Ita

Ana ba da ita kafin a fita zuwa Sallar Idi ko kafin Ranar Sallah da kwana daya ko biyu. Abin da ake bayarwa shi ne Muddan Nabiyy (mudun awo ne dan madaidaici wanda za a iya auna shi da cikin tafukan hannun mutum mai matsakaicin tsawo) guda hudu a kan kowane mutum. Ana fitarwa daga dukkan nau’in abinci, kamar mu a nan mu ce shinkafa, masara, doya, dawa, dauro, cukwi, nono da duk dai abin da galibin mutane suke amfani da shi a matsayin abinci.

Malaman kasar Maroko wadda kasa ce ta Malaman Musulunci kuma ‘yan’uwanmu ne Malikawa; sun yi fatawa cewa ya halasta a ba da kudi a madadin abinci a Zakkar. Za a kimanta kudin adadin Muddan Nabiyy hudu da za a fitar sai a ba da. Wannan ya halasta.

Idan mutum ya yi nazarin hikimar ba da Zakkar, wato wadata talakawa da miskinai don kar a gan su suna bara saboda rashin abincin da za su ci a Ranar Sallah, wannan kudin da za a ba su sai ya fi musu dadi a kan tsabar abincin. Domin wani idan ka bashi hatsin watakila ba zai iya nikowa ba, toh ka ga shi a wurinsa kudin zai fi masa amfani fiye da dawa ko masara. dan dama-dama shinkafa ko doya wanda duk za a iya dafawa ba sai an nika ba. Amma fa a lura, kowane irin abinci mutum ya bayar ya yi. Saboda amfanin kudin ne ya sa muka kawo wadannan bayanan.

An fi so a ba da Zakkar ga mutanen kirki daga cikin talakawa ko wadanda suke da almajirai a hannunsu wadanda idan an ba su ba za su je bara ba a ranar. Ita Shari’a ba ta so a ga kaskancin mutum a wannan ranar, so ake kowa ya nuna girman Musulunci, kodayake wasu ‘yan’uwa ba za su yarda ba, duk abin da aka ba su ba za su iya hakura ba sai sun fita bara. Toh amma kuma kar wannan ya sa a ce ba za a ba su ba.

Idan mutum ya fitar da Zakkar sai ya kasance babu miskinai a kusa da shi da zai ba su, to ya dauka ya kai wurin da suke ya ba su, kar ya ce ai tunda babu miskinai a kusa da shi shikenan ba sai ya ba da ba.

Fa’ida: hatta kafirin da ake zaune da shi in talaka ne za a iya ba shi Zakkar don ya wadata a wannan ranar. So ake dan Adam ya zama ya wadata saboda albarkar ranar ta Sallah.

Sallar Idi

Sallar Idin Shan Ruwa (karamar Sallah) da Sallar Idin Layya (Babbar Sallah kamar yadda galibin Hausawa ke cewa), an shar’anta su a Musulunci a shekarar farko da yin Hijirar Annabi (SAW) daga Makka zuwa Madina. Kuma Annabi (SAW) ya dauwama a kansu (yana aikatawa). Ya hori maza da mata da yara da manya su fita zuwa gare su, ma’ana su je Masallacin Idi.

Ana so a yi wanka, a sa turare, a sanya mafi kyan tufafi da mutum yake da shi. A Sallar Idin Shan Ruwa, ana so a ci abinci kafin a fita zuwa Masallaci koda dabino ne ko shayi. Ana so a dan jinkirta ta kadan; savanin Sallar Idin Layya da aka fi so a jinkirta cin abinci har sai an dawo. Idan mutum ya samu ikon yin Layya; ana so ya bude baki da naman Layyar sannan an fi so a gaggauta yin ta domin a dawo gida a yi Layya.

Ba a yin Sallar Idi (duka biyun) a Rufaffen Masallaci sai dai in akwai lalura kamar ta ruwan sama. A wajen gari ake fita yin SallarIdodin biyu ko kuma duk filin da aka samu. Annabi (SAW) bai tava yin Sallar Idi a Rufaffen Masallaci ba sai sau daya saboda ruwan sama kamar yadda Hakim ya ruwaito Hadisin.

Ana so a canja hanyar da aka je Masallacin Idi wajen dawowa amma ba dole ba ne. Ana so a yi Sallar Idin Shan Ruwa kamar da misalin karfe bakwai da rabi na safe (7:30am), Sallar Layya kuma kamar da misalin karfe bakwai na safe (7:00am). Amma ko sun kai karfe goma sha daya na rana babu laifi, duk lokacin yin su ne.

Ba a yin Kiran Sallah ko Ikamah ko cewa “a tashi a yi sallah”. Da zarar Sarki ko wanda ya tsaya a matsayinsa ya iso filin masallaci sai a mike a shiga Sallah. A raka’ar farko; bayan Kabbarar Harama sai a kara Kabbara shida, sun zama bakwai kenan. A raka’a ta biyu; bayan Kabbarar Tasowa daga Sujuda sai a kara Kabbara biyar, sun zama shida kenan. Ba a yin Nafila kafin Sallar Idi (duka biyu) kuma ba a yi a bayanta. Liman zai yi huduba bayan an yi sallama, wanda yake so zai zauna ya ji wanda wani uzuri ya kama shi sai ya tashi ya tafi ba tare da ya yi magana (surutai) ba.

Ana so a yi wasanni, da kade-kade, da wake-wake, da ciye-ciye, da nishadi, da ziyarori, da yi wa juna murnar Idi. Ana so a yi kallon wasannin ko rawar da ake yi, duk ya halatta a wannan ranar. Wannan shi ne Musulunci sassauka kamar yadda Annabi (SAW) ya fada, Tirmizhi da Ibn Majah da Baihaki suka fitar.

Allah ya sa mu kammala Azumi lafiya, mu yi Sallah lafiya, ya hore wa dukkan Musulmi abin da za a yi hidimomin Sallah da shi, Allah ya karva mana ibadunmu kuma ya karve mu da falalarsa albarkar Annabi (SAW).

 

‎Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadi wa ala alihi hakka kadrihi wa mikdarihil aziym.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dausayin MusulunciZakkah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya

Next Post

Dantsoho Ya Nemi Masu Zuba Hannun Jari Da Su Ci Gajiyar Tsarin EPT Na NPA

Related

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

4 days ago
An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa
Addini

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

6 days ago
Nijeriya Za Ta KarÉ“i Bakuncin Gasar Karatun AlÆ™ur’ani Mai Girma Ta Duniya
Addini

Nijeriya Za Ta KarÉ“i Bakuncin Gasar Karatun AlÆ™ur’ani Mai Girma Ta Duniya

2 weeks ago
Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
Addini

Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025

1 month ago
Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhanin Rasuwar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi 
Addini

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhanin Rasuwar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi 

1 month ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da É—umi-É—uminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

1 month ago
Next Post
Dantsoho Ya Nemi Masu Zuba Hannun Jari Da Su Ci Gajiyar Tsarin EPT Na NPA

Dantsoho Ya Nemi Masu Zuba Hannun Jari Da Su Ci Gajiyar Tsarin EPT Na NPA

LABARAI MASU NASABA

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.