• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Sun Yi Awon Gaba Da Mata Da Yara A Garin Jere
  • MazanDa Aka Kama Suka Kubuta Sun Yi Bayani Dalla-dalla

“A ranar da abin zai faru, Auwal ya kai amaryarsa Rabi’atu asibitin Unguwar Masukwani tun da safe saboda laulayin juna biyu da take da fama da shi. Da yamma bayan Isha’i dan’uwansa Rabi’u ya ziyarce shi tare da matarsa Aisha. Suka dan jima suna hira, zuwa can Rabi’u ya ce dare ya fara yi bari su tashi su koma sashinsu.

Sun tafi ba da dadewa ba, Auwal yana kwance a tabarma a tsakiyar falonsu ita kuma amaryarsa tana zaune a kujera suka ci gaba da hira, kwatsam sai ga ‘yan bindiga suka shigo musu, to dama ba su rufe kofa ba saboda dare bai yi ba sosai. Suka ce ka tashi mu tafi, ya ce babu inda zan je, sai suka ce to za mu tafi da kai da matarka ya ce babu inda za mu je, to a wannan lokacin ya mike tsaye ya tare kofar shiga falon, kawai sai suka harbe shi a hannu!

  • 2023: Ni Kadai Ne Zan Iya Kawo Kuri’un Da Za Su Kayar Da Atiku —Rochas

“Hannun ya yi kamar an kwankwatsa da adda, ‘yar fata ce kawai take rike da shi. Suka yi yunkurin fitar da matar ya sake ce musu babu inda za ku je da ita, daga nan ne suka harbe shi a ciki, harbi uku suka yi masa. Nan take ya fadi cikin jini sai suka tafi da matar. To duk abin da ake yi akwai kaninsa Barde yana daki yana ji amma ba hali ya fita, da (Barde) ya ji (‘yan bindigar) sun fita shi ne ya fito da gudu cikin gida ya yi ihu ya ce sun kashe Danlami (Auwal).

Nan fa mutanen gida aka fiffito, to hatta lokacin da mutane suka zo duk da halin da angon yake ciki amma yana cewa ku daga ni, sun tafi da matata, ku daga ni har dai bakinsa ya rufu ya kasa magana.” Wannan shi ne takaitaccen jawabin da majiyarmu ta yi game da kisan da ‘yan bindiga suka yi wa wani ango Auwal Isah suka kuma tafi da amaryarsa Rabi’atu mai dauke da juna biyu a garin Jere da ke babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna, yankin Karamar Hukumar Kagarko a ranar Juma’a da dare.

Karo na uku kenan da ‘yan bindiga ke shiga cikin garin Jere suna sace mutane. Na farko sun yi a Unguwar Cabiho inda suka sace wani matashi sai da aka ba su kimanin Naira Miliyan 20, na biyu a Unguwar Ma’aji, sun sace sama da mutum bakwai sai da aka ba su kimanin Naira miliyan 25 har da mashuna guda uku, bayan sun kashe mutum biyu a cikin wadanda suka sace a can inda suke garkuwa da su.

Labarai Masu Nasaba

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

Kwata-kwata bai fi wata daya da sako mutanen da suka sace a karo na biyu ba, suka kuma dawowa suka kutsa har tsakiyar garin suka kashe ango, suka tafi da amaryarsa, suka sace mata da yara a gidan tsohon Kwamishinan Yaki da Fatara na Jihar Kaduna wanda yake shugaban Jam’iyyar PDP na Karamar Hukumar Kagarko, Hon. Abdulrahman Ibrahim da aka fi sani da ‘Apo’.

A cewar majiyarmu, “Barayin sun shiga gidan Hon. Abdulrahman dare bai ma wani yi sosai ba a lokacin don bai wuce karfe 11 ba. Ikon Allah, duk sauran matansa sun rufe kofa sai Hajiya Ladidi kawai, ita kuma ba ta rufe ne ba saboda akwai bakin da suka zo bikin aure za su kwana a wurinta.

To akwai wasu yara maza da suke kallo a dakinta, amma da ‘yan bindigar suka zo sun samu sun silale ta kofar kicin ta baya. Sai suka tafi da matarsa Hajiya Ladidi da ‘yarta ta goye, da kanwarsa Rabi’atu da ta zo bikin auren daga Zariya, da kanwar matar da suke kira da Walidah.”
Har ila yau, majiyar tamu ta bayyana cewa, barayin sun yi yunkurin shiga gidan Yariman Jere, Alhaji Abdulkarim amma ba su samu nasarar balle kofar gidansa ba.

Wakazalika, wata majiya ta ruwaito mana cewa, barayin sun kutsa cikin garin ne ta hanyar Kasuwa Sabo, inda suka yi awon gaba da wani maishayi Malam Yakubu da wani da ya zo shan shayi da ake ce wa Baba Isah sai kuma wani matashin magidanci mai suna Mubarak.

Da yake bayyana mana yadda ya yi arba da barayin, Malam Mubarak ya ce, “Ina kan hanyata ta dawowa daga can babban gidanmu, daidai bayan dogon gini ina haska tocin wayata, kusa da katangar gidan Alhaji Abba, kawai sai na ji an ce zo nan, ina matsowa suka kama kwalar rigata suka tsugunar da ni tare da su Yakubu da aka kama. Can dai Allah ya ba ni kwarin gwiwa da na ji zan iya sabule rigar, kawai sai na mike na zura a guje. Daya daga cikin barayin, shi ne katon cikinsu ya bi ni muka rufa a guje, to sai magazine (sinkin alburushi) dinsa ta fadi, shi ne na shiga wani gida da gudu na ce wa samarin da na tarar a zauren gidan su gudu ga ‘kidnappers’ nan. Suka shigo da gudu bayan sun rufe kofa, na yi tsalle na kama katangar gidan zan tsallaka kawai sai saman katangar ya rufto mun. To sai na ji shi wanda ya biyo ni din ya harba bindiga ya koma. Shi ne na samu na fito na karaso gida.” In ji shi.

An ruwaito cewa Shugaban ‘Yansanda na Babban Ofishin Shiyyar Jere, ACP Umar Faruk ya kira sojoji da ke Katari domin su kawo dauki, sai dai mutanen garin sun ce babu wani abin a zo a gani da suka tabuka, domin ‘yan bindigar ba su jima da tafiya da mutanen ba amma suka ki bin su sai dai harbe-harben da suka rika yi a sama kawai.

Da yake mana karin haske kan lamarin, wani dankasuwa a Jere Malam Muntari, ya bayyana cewa “daya daga cikin wadanda aka kama Malam Yakubu ya ce sojojin sun je can wurin hanyar jirgin kasa kamar dai suna so su shawo kan barayin, amma a banza, harbi kawai suka yi ra-ta-ta-ta-ta. Daga nan barayin suka ce kowa ya kwanta (su da wadanda suka sace), kuma suka ce a yi baya, ma’ana a sauya hanya.”
Bugu da kari, wani da darayin suka sako washegari, ya bayyana cewa, daya daga cikin matan da suka kama, kafafuwanta na ta jini sai da ya cire rigarsa ya barke ya ba ta don ta nade a kafa. Ya ce tun da aka kama su, barayin suka ba shi yarinyar da ake shayarwa ya saba ta. Sun je wani wuri suna hutawa sai ogan cikinsu ya ce masa ya kama hanya ya tafi.

Mun yi kokarin jin ta bakin ‘yansanda game da abin da ya faru, sai dai ba su bayar da wani bayani ba, domin mun kira Babban Kwamandan Shiyya na Jeren, ACP Umar Faruk ya ce a tuntubi Jami’in hulda da jama’a na rundunarsu ta Jihar Kaduna har ma ya aiko mana da lambar wayarsa. Sai dai mun yi ta kira wayar ba ta shiga. Sannan mun tura sakon way ana tes shi ma shiru. Haka nan wakilinmu na Kaduna Shehu Yahaya ya neme shi inda ya ce masa yana cikin taro amma idan ya fito zai yi masa magana, har zuwa lokacin kammala rubuta wannan rahoto dai shiru.

Wata majiya daga ‘yansandan ta tabbatar mana da sunayen wadanda suke hannun ‘yan bindigar da suka hada da Laurat Abdulrahman, Safiyah Abdulrahman, Rabi’at Ibrahim, Rabi’at Abubakar Zakariyya (amaryar da mijinta ya yi shahada) da Walidah Surajo Musa, dukkansu mata da yara.

Da suke gabatar da jawabi a wurin jana’izar marigayi Auwal Isah, wasu daga cikin Malaman Jere, Imam Abdulrahman Musa da Imam Ibrahim Tahir da Malam Ibrahim Zakari, sun karfafa gwiwar al’ummar garin su mike tsaye wajen bayar da gudunmawa kan sha’anin tsaron garin, inda suka yi kiran kara sa ido sosai a kan bakin fuska da gyara tarbiyyar yara da kuma kara himma ga addu’o’i.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Sin Ta Baiwa Afrika Da Duniya Gagarumar Gudunmawar Wanzar Da Zaman Lafiya

Next Post

Lokaci Ya Yi Da Nima Zan Zama Shugaban Kasa, Na Gaji Da Yi Wa Wasu Hidima —Tinubu

Related

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
Labarai

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

2 hours ago
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO
Labarai

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

3 hours ago
An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda
Manyan Labarai

An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

5 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
Tsaro

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

7 hours ago
Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja
Labarai

Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

9 hours ago
Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

10 hours ago
Next Post
Lokaci Ya Yi Da Nima Zan Zama Shugaban Kasa, Na Gaji Da Yi Wa Wasu Hidima —Tinubu

Lokaci Ya Yi Da Nima Zan Zama Shugaban Kasa, Na Gaji Da Yi Wa Wasu Hidima —Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

May 28, 2025
An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

May 28, 2025
Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.