ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Nima Zan Zama Shugaban Kasa, Na Gaji Da Yi Wa Wasu Hidima —Tinubu

by Muhammad
4 years ago
Lokaci

Jagoran jam’iyyar APC na kasa kuma dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis, ya gargadi wakilan jam’iyyar daga jihar Ogun da su mara masa baya a babban taron jam’iyyar na kasa mai zuwa zuwa na zaben shugaban kasa na shekarar 2023.

Tinubu, wanda ya yi jawabi ga wakilan jam’iyyar a Abeokuta, babban birnin jihar, yana mai jaddada cewa lokaci ya yi da ya kamata ya ci ribar ayyukansa da sadaukarwa wajen gina babbar jam’iyyar siyasa.

  • ‘Yan APC A Legas Sun Yi Zanga-zanga Kan Zargin Tinubu Da Kakaba Musu ‘Yan Takara

Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, ya fito ne daga jihar Ogun.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar APC na kasa ya tunatar da cewa ya marawa ‘yan siyasar Nijeriya da dama baya don ganin sun cimma burinsu na siyasa, inda ya bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari na daya daga cikin irin mutanen da ya goyawa baya.

Ya kuma bayyana cewa irin su Nuhu Ribadu da Atiku Abubakar a lokacin da tsofaffin jam’iyyunsu na siyasa suke ya yi musu hidima, ya kuma bayyana cewa a baya ya samar da tsarin siyasa da dama don tsayawa takarar shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Tinubu ya bayyana cewa bai taba yin nadamar sadaukarwar da ya yi wa Osinbajo ba, ta damar da ya ba shi ta zama mataimakin shugaban kasa ga shugaba Buhari ba, a yayin da ake shirin tunkarar zaben shugaban kasa na 2015.

“A yanzu sama da shekaru 25 ina bautar wadannan ’yan siyasa maza da mata, har ma da Shugaban kasa,”

“Ban da irin gudunmawarmu da Buhari bai samu nasarar lashe wancan zaben na shugaban kasa a 2015 ba bayan yunkurin da ya yi sau uku ba tare da goyon bayana ba”.

“Tun da Shugaba Buhari ya hau mulki ban karbi mukamin minista ko jakadanci ba, amma yanzu lokaci na ne, goyon bayana ga wadannan ‘yan siyasa maza da mata ya isa, ba na son shiga cikin tarihin siyasa mai ban tausayi a cikin Najeriya, na zo ne domin neman kuri’un ku.”

Lokaci
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Zaben Atiku: Muna Jan Kunnen Buhari Da APC Kan Matsalolin NDDC – Samarin APC A Neja-Delta

Yayin Da Atiku Ya Zama Kwamandan PDP A 2023…Kallo Ya Koma APC

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.