• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da sannu a hankali fasahar zamani na Artificial Interligent na neman mamaye yadda bankuna da cibiyoyin kudi ke gudanar da harkokinsu, a kan haka ‘yan Nijeriya da masana ke bayyana tsoron su na yiwuwar karuwar harkokin ‘yan damfara da cuwacuwa saboda dogaro da wannan fasahar, masu hulda da bankuna da bankunan su kansu za su ci gaba da tafka asarar makudan kudade kamar yadda binciken jaridar LEADERSHIP ya nuna.

Wannan na faruwa ne a daidai lokacin da Nijeriya ke asarar dala miliyan 500 sakamakonm sata ta intanet, wanda hakan ke nuna kudin ya kai Naira biliyan 675 a duk shekara inda ka yi amfani da canjin naira 1,350 a kan dala 1.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Da Ɗumi-ɗumi: EFCC Za Ta Gurfanar Da Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama Da ‘Yarsa A Gobe Alhamis

Kididdga daga hukumar sadarwar Nijeriya NCC ya nuna cewa, Nijeriya na asarar kudaden da aka ambata ne a bangarori daban-daban yayin da bangaren bankunan Nijeriya ya yi asarar fiye da Dala biliyan 8 ga ayyukan masu zamba ta intane a shekarar 2022 kawai.

Hukumar sadarwar ta bayyana cewa, kashi 71 kawai ne bankuna ke bayar da rahoton harin da ake kai musu ta intanet, amma hukumar kula da harkokin bankuna a Nijeriya ‘Nigeria Interbank Bank Settlement System (NIBSS), ta sanar da cewa, bangaren bankuna a Nijeriya sun yi asarar fiye da naira biliyan 50.5 ga masu zamba ta intanet a tsakanin shekarar 2019 zuwa 2023.

Fasahar zamani na musamman da ake kira da ‘Artificial Intelligence (AI)’ fasaha ce da ake tafiyar da harkoki tamkar irin na dan adam, an shirya na’ura ta yadda za ta rinka aikin yau da kullum na banki tamkar dan adam kuma a cikin sauri.

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Duk da cewa, wannan fasahar ta AI abu ne mai kyau ga bangaren bankuna, inshora da sauran harkokin kudi amma matsalar ita ce yadda za a kare bayanai da kuma sirrukan masu hulda.

Babban damuwar al’umma anan shi ne yadda wasu bayanai na sirri na al’umma da za a iya sanya wa fasahar AI za su iya fadawa hannun bata gari ta yadda za su iya amfani da su wajen damfarar masu hulda da wadnnan cibiyoyin kudi, ba tare da sun sani ba.

A kan haka aka gargadi ‘yan Nijeriya da su yi hattara da irin manhajojin AI da suke saukewa a wayoyinsu don su kan kasance wasu kafa na lekan asiri da bata gari ke amfani da su wajen satar bayanai masu muhimmanci daga wayoyin mutane domin aikata muggan ayyukansu na damfara.

Hukumar Lamuni ta Duniya IMF, ta bayyana cewa, cibiyoyin kudi sun sanar da asarar kudaden da ya kai dala biliyan 12 tun daga shekarar 2004 da kuma asarar dala biliyan 2.5 tun daga shekarar 2020.

A rahotonta na halin da bangaren harkar kudi na duniya yake tafiya na shekarar 2024, IMF ta bayyana cewa, hare-hare ta intanet ga bankuna yana kara karuwa a kullum, inda ake asarar kudade masu dimbin yawa.

Masana sun bayyana cewa, masu aikata laifi ta inatne sun rungumi tsarin AI, inda suka fito da sabbin dabaru na rudar da mutane inda suke amfani da jimloli masu tsawo waje aikata damfara musamman ga bankuna a fadin duniya.

A yayin da ake ci gaba sauraron aukuwar karin hare-haren na ‘yan damfara masu amfani da AI, masana sun bayar da shawarar, a karfafa dabarun kariya ga manhajojin bankuna masu AI tare da kuma sabunta su aka-akai.

Rahoto na baya-bayan nan daga cibiyar binciken laifukkan da ake aikatawa da kwamfuta, ‘Computer Crime Research Centre (CCRC)’ ta yi lura da cewa, damfara ta intanet ya haura zuwa akalla dala tiriliyan 12 a shekrar 2024 saboda amfani da fasahar AI, rahoton ya kara da cewa, “A shekarun 2024 da 2025, za mu fuskanci karuwar ayyukan ‘yan damfara ta intanet masu kai hari ga bankuna, za kuma mu ga karuwar amfani da fasahar AI wajen aitaka wadanna ayyukan rashin gaskiyar.

“Fasahar Deepfake zai mamaye tsofaffin hanyoyin da ‘yan damfara ke amfani dasu. Yayin da harkokin kasuwanci da dama za su rungumi fasahar AI, za kuma su fuskanci gaggarumar barazana daga masu aikata laifukka ta intanet musamman amfani da fasahar AI, wadanda za su bullo da sabbin fasahohi da za su karya duk wata kariya da cibiyoyin kudin ke samarwa.

“Bangaren da za su fi fadawa wannan hadarin sun hada da masu kananan kasuwanci da cibiyoyin kudi da basu da manyan jari wadanda ba za su iya saye tare da samar wa kan su manhajoji masu karfi da za su bayar da kariyar da ake bukata ba,” in ji rahoton.

Da yake tabbatar da sakamakon wannan rahoton, wani tsohon darakta a hukumar NDIC, Dakta Jacob Afolabi, ya lura da cewa, an samu karuwar hare-hare ga cibiyoyin kudi ta hanyar fasahar AI a shekarar 2023, sun kuma aukar da gaggarumin asara ga cibiyoyi da hukumomin gwamnati.

Afolabi ya kuma yi bayanin cewa, fasahar AI na iya sarrafa bayanai masu yawan gaske a lokaci daya, abin da yake kara tsoron kariya ga sirrin wadanan bayanai da kuma tsaronsu.

“Fasahar Al na kara karuwa tare da sarkakiya, haka kuma kare masu amfani da su yake kara wahala ga kuma yiwuwar an yi amfani da su ta barauniyar hanya yana kara karuwa. Masu aikata laifukka ta intanet na kara fito da sabbin hanyoyin da za su karya duk wata kariya da aka yi wa fasahar AI don su cutar da masu amfani da ita musamman a bangaren cibiyoyin kudi da sauransu,” in ji shi.

Domin samar da kariya ga bayanan al’umma, Afolabi ya bayar da shawarar a samar da dokoki na musamman domin kariya ga masu amfani da fasahar AI.

Dogaro kacikan ga fasahar AI yana kaiwa ga rasa zimma daga nutane, tunani mai amfani da kuma rasa hannun dan adama abin da ake yi, a kan haka tsohon daraktan ya bayar da shawarar cewa, ya kamata a samar da daidaito a tsakanin amfani da fasahar AI da kuma amfani da dan adama a harkokin bankuna da wuraren da ake amfani da fasahar AI saboda samar da kariya da kuma sanya ido na dan adam a harkokin yau da kullum.

Ya kuma kara da cewa, “rungumar fasahar AI na iya haifar da rasa ayyukan yi ga al’umma a ma’aikatu musamman ga ma’aikatan da basu da kwarewa na musamman, dole ma’aikata su rungumi ilimin fasahar zamani in har suna son kasancewa a fagen ayyuka a wannan zamani,”.

Haka kuma darakta mai kula harkokin gwamnati a kamfanin Microsoft Africa, Akua Gyekye, ya ce in har ana son amfani da fasahar AI a cikin nasara dole hukumomin gwamnati su rungumi tsarin tare da samar da tsarin gudanar da ayyukan a hukumance.

Ya bayyana cewa, kasashen Afrika da dama sun fara samar da dokoki da tsare-tsare a hukumance a kan tafiyar da fasahar AI, hakan ya kuma kai ga shirye-shiryen samar da wani tsari da zai tafiyar da hanyoyin kariya ga fasahar AI a duniya gaba daya.

Ta kuma kara da cewa, Kungiyar Tarayyar Afrika ta kira taron masana kimiyyar sadarwa a wannan shekarar inda suka samar da daftarin dokoki na yadda za a tafiyar da harkokin fasahar AI a tsakanin kasashen Afrika.

Wani jami’i a hukumar sadarwa ta Nijeriya NCC, Kelechi Nwankwo, ya ce, duk da bunkasar harkokin sadarwar zamani a Nijeriya, ana fuskantar hare-hare na intanet abin kuma na iya karuwa a nan gaba.

Da yake nuna damuwarsa, shugaban kamfanin inshora na Guinea Insurance Plc, Ademola Abidogun, ya ce, duk da cewa, amfani da fasahar AI na da muhimmanci ga bangaren inshora amma matsalolin da ke tattare da hakan suna da yawan gaske, musamman a bangaren kariya ga bayanai na sirri na al’umma.

Tun da farko hukumar Lamuni ta Duniya IMF ta bayyana cewa, masu aikata laifi ta intanet sune babbar barazana ga harkokin cibiyoyin kudi inda suke dagula harkokin bankuna suna kuma sanya tsoro ga masu hulda da cibiyoyin kudin gaba daya.

Domin karfafa bangaren bankuna da cibiyoyin kudin, IMF ta bayar da shawara ga manyan bankuna kasa na su samar da tsarin kasa na yaki da masu zamba ta intanet tare da sanya ido da kuma aiwatar da dukkan dokokin da aka samar na kariya daga sharrin masu aikata zamba ta intanet.

Haka kuma, a nasa tsokacin, shgaban kungiyar jami’an kula da tsaron bankuna a Nijeriya (CCISONFI), Mr. Festus Amede, ya bayyana bukatar samar da tsarin kariya ga bayanan sirri a cibiyoyin kudin kasar nan musamman daga barazanar masu aikata laifi ta intanet.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

Next Post

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

1 day ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

1 day ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

1 day ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

LABARAI MASU NASABA

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.