• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Amfanar Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Amfanar Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan kammala taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC a kwanan baya, masu fashin baki ke ta yin tsokaci game da tasirin dake tattare da dorewar hadin gwiwar Sin da kasashen nahiyar Afirka.

Da ma dai cikin sama da shekaru 70 da suka gabata, sassan biyu sun wanzar da dangantaka da abota da hadin kai a fannoni daban daban, wanda hakan ya haifar da sakamako mai gamsarwa. Kaza lika a shekarun baya bayan nan an ga yadda hakan ya ingiza hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Afirka zuwa matsayin koli, ta yadda ake hasashen dukkanin ci gaban da kasar Sin ta samu na iya yin tasiri mai kyau ga ci gaban kasashen Afirka baki daya.

  • Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou
  • Yawan Mutanen Da Suka Shiga Da Fita Daga Kasar Sin A Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Ya Zarce Miliyan 5.25

Yanzu haka dai kasar Sin ce kan gaba wajen yawan jari da sassan waje ke zubawa a kasashen Afirka, kana ita ce babbar abokiyar huldar cinikayya ta kasashen Afirka cikin shekaru 15 a jere. Wata kididdiga ma ta nuna yadda tsakanin shekarar 2000 zuwa 2023, adadin darajar cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta karu daga kimamin yuan biliyan 100 zuwa tiriliyan 1.98, wanda hakan ke nuna karuwar kimamin kaso 17.2 bisa dari a duk shekara.

Wannan a fannin cinikayya da zuba jari ke nan. Wani fannin kuma mai matukar muhimmanci shi ne na bunkasa hada-hadar harkokin tattalin arziki da kudade, wanda suka kunshi samar da lamuni mai saukin ruwa, da tallafin jin kai, da gudanar da ayyukan samar da ababen more rayuwa bisa hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, wanda ko shakka babu ya sanya kasar Sin samun karin karbuwa tsakanin kasashen Afirka.

Bugu da kari, kasar Sin na mu’amala da kasashen Afirka bisa kare ’yancinsu na zabar hanyar neman bunkasuwa mafi dacewa da su, tare da cimma nasara bisa burikansu. Ya zuwa wannan lokaci, kamfanonin Sin sun gina tare da gyara sama da layin dogo da tsayinsa ya kai sama da kilomita 10,000, da hanyoyin mota masu tsayin kusan kilomita 100,000, da gadoji kusan 1,000, da kusan tashohin ruwa 100, baya ga turakun lantarki masu tsayin kusan kilomita 66,000, da manyan turakun sadarwa da tsayinsu ya kai kilomita 150,000 a sassan kasashen Afirka daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Masharhanta na ganin irin wadannan manyan ayyukan raya kasa dake gudana karkashin manufofin samar da ci gaba na Sin irin su shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI, muhimman ginshikai ne dake kara dunkule nahiyar Afirka waje guda, da fadada hadewarta da sauran sassan duniya, ta yadda al’ummun Sin da na nahiyar Afirka za su cimma nasarar zamanantar da kansu, da kuma kaiwa ga gina al’ummar bai daya ta Sin da Afirka mai kyakkyawar makoma guda. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou

Next Post

Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

Related

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

18 hours ago
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

19 hours ago
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
Daga Birnin Sin

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

20 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

21 hours ago
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

22 hours ago
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

23 hours ago
Next Post
Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.