• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Amfanar Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Amfanar Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan kammala taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC a kwanan baya, masu fashin baki ke ta yin tsokaci game da tasirin dake tattare da dorewar hadin gwiwar Sin da kasashen nahiyar Afirka.

Da ma dai cikin sama da shekaru 70 da suka gabata, sassan biyu sun wanzar da dangantaka da abota da hadin kai a fannoni daban daban, wanda hakan ya haifar da sakamako mai gamsarwa. Kaza lika a shekarun baya bayan nan an ga yadda hakan ya ingiza hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Afirka zuwa matsayin koli, ta yadda ake hasashen dukkanin ci gaban da kasar Sin ta samu na iya yin tasiri mai kyau ga ci gaban kasashen Afirka baki daya.

  • Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou
  • Yawan Mutanen Da Suka Shiga Da Fita Daga Kasar Sin A Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Ya Zarce Miliyan 5.25

Yanzu haka dai kasar Sin ce kan gaba wajen yawan jari da sassan waje ke zubawa a kasashen Afirka, kana ita ce babbar abokiyar huldar cinikayya ta kasashen Afirka cikin shekaru 15 a jere. Wata kididdiga ma ta nuna yadda tsakanin shekarar 2000 zuwa 2023, adadin darajar cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta karu daga kimamin yuan biliyan 100 zuwa tiriliyan 1.98, wanda hakan ke nuna karuwar kimamin kaso 17.2 bisa dari a duk shekara.

Wannan a fannin cinikayya da zuba jari ke nan. Wani fannin kuma mai matukar muhimmanci shi ne na bunkasa hada-hadar harkokin tattalin arziki da kudade, wanda suka kunshi samar da lamuni mai saukin ruwa, da tallafin jin kai, da gudanar da ayyukan samar da ababen more rayuwa bisa hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, wanda ko shakka babu ya sanya kasar Sin samun karin karbuwa tsakanin kasashen Afirka.

Bugu da kari, kasar Sin na mu’amala da kasashen Afirka bisa kare ’yancinsu na zabar hanyar neman bunkasuwa mafi dacewa da su, tare da cimma nasara bisa burikansu. Ya zuwa wannan lokaci, kamfanonin Sin sun gina tare da gyara sama da layin dogo da tsayinsa ya kai sama da kilomita 10,000, da hanyoyin mota masu tsayin kusan kilomita 100,000, da gadoji kusan 1,000, da kusan tashohin ruwa 100, baya ga turakun lantarki masu tsayin kusan kilomita 66,000, da manyan turakun sadarwa da tsayinsu ya kai kilomita 150,000 a sassan kasashen Afirka daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Masharhanta na ganin irin wadannan manyan ayyukan raya kasa dake gudana karkashin manufofin samar da ci gaba na Sin irin su shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI, muhimman ginshikai ne dake kara dunkule nahiyar Afirka waje guda, da fadada hadewarta da sauran sassan duniya, ta yadda al’ummun Sin da na nahiyar Afirka za su cimma nasarar zamanantar da kansu, da kuma kaiwa ga gina al’ummar bai daya ta Sin da Afirka mai kyakkyawar makoma guda. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou

Next Post

Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

9 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

10 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

12 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

12 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

14 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

15 hours ago
Next Post
Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.