ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Amfanar Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Tun bayan kammala taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC a kwanan baya, masu fashin baki ke ta yin tsokaci game da tasirin dake tattare da dorewar hadin gwiwar Sin da kasashen nahiyar Afirka.

Da ma dai cikin sama da shekaru 70 da suka gabata, sassan biyu sun wanzar da dangantaka da abota da hadin kai a fannoni daban daban, wanda hakan ya haifar da sakamako mai gamsarwa. Kaza lika a shekarun baya bayan nan an ga yadda hakan ya ingiza hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Afirka zuwa matsayin koli, ta yadda ake hasashen dukkanin ci gaban da kasar Sin ta samu na iya yin tasiri mai kyau ga ci gaban kasashen Afirka baki daya.

  • Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou
  • Yawan Mutanen Da Suka Shiga Da Fita Daga Kasar Sin A Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Ya Zarce Miliyan 5.25

Yanzu haka dai kasar Sin ce kan gaba wajen yawan jari da sassan waje ke zubawa a kasashen Afirka, kana ita ce babbar abokiyar huldar cinikayya ta kasashen Afirka cikin shekaru 15 a jere. Wata kididdiga ma ta nuna yadda tsakanin shekarar 2000 zuwa 2023, adadin darajar cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta karu daga kimamin yuan biliyan 100 zuwa tiriliyan 1.98, wanda hakan ke nuna karuwar kimamin kaso 17.2 bisa dari a duk shekara.

ADVERTISEMENT

Wannan a fannin cinikayya da zuba jari ke nan. Wani fannin kuma mai matukar muhimmanci shi ne na bunkasa hada-hadar harkokin tattalin arziki da kudade, wanda suka kunshi samar da lamuni mai saukin ruwa, da tallafin jin kai, da gudanar da ayyukan samar da ababen more rayuwa bisa hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, wanda ko shakka babu ya sanya kasar Sin samun karin karbuwa tsakanin kasashen Afirka.

Bugu da kari, kasar Sin na mu’amala da kasashen Afirka bisa kare ’yancinsu na zabar hanyar neman bunkasuwa mafi dacewa da su, tare da cimma nasara bisa burikansu. Ya zuwa wannan lokaci, kamfanonin Sin sun gina tare da gyara sama da layin dogo da tsayinsa ya kai sama da kilomita 10,000, da hanyoyin mota masu tsayin kusan kilomita 100,000, da gadoji kusan 1,000, da kusan tashohin ruwa 100, baya ga turakun lantarki masu tsayin kusan kilomita 66,000, da manyan turakun sadarwa da tsayinsu ya kai kilomita 150,000 a sassan kasashen Afirka daban daban.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Masharhanta na ganin irin wadannan manyan ayyukan raya kasa dake gudana karkashin manufofin samar da ci gaba na Sin irin su shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI, muhimman ginshikai ne dake kara dunkule nahiyar Afirka waje guda, da fadada hadewarta da sauran sassan duniya, ta yadda al’ummun Sin da na nahiyar Afirka za su cimma nasarar zamanantar da kansu, da kuma kaiwa ga gina al’ummar bai daya ta Sin da Afirka mai kyakkyawar makoma guda. (Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
Next Post
Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.