• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Asibitin Ƙauran Namoda Da Ya Inganta

by Leadership Hausa
1 year ago
gwamna

A ranar Talatar nan ne Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda, wanda aka yi masa gyara, tare da wadata shi da kayan aikin kula da lafiya.

Babban asibitin, yana kula da Ƙauran Namoda da maƙwabtanta, wanda kuma aka wadata shi da kayan aiki don ya samar da iingantacen kiwon lafiya.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa babban asibitin, an samar masa da kayan aikin kula da lafiya, waɗanda suka haɗa da na’urorin binciken cututtuka, gadajen haihuwa, na’urar auna bugun zuciya (ECG), na’urorin binciken jini, babbar na’urar binciken jini ta ‘automatic hematology analyzer’, na’urar auna nauyi ta zamani, fitilar haskawa yayin aikin tiyata da dai wasu kayan kula da lafiya da daman gaske.

Sanarwar ta ƙara da cewa, asibitocin gaba ɗaya na da matuƙar muhimmanci wajen samar da ingantaccen kiwon lafiya, wanda ya kamata ya zama mai sauƙi ga al’ummar Jihar Zamfara.

A wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya nanata cewa babban abin da gwamnatinsa ta mayar da hankali a kai shi ne farfaɗo da taɓarɓarewar ababen more rayuwa da magance matsalolin da ke addabar dukkanin sassan tattalin arzikin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

gwamna

“Wannan hangen nesa ya sa muka yanke shawarar samar da ajandar kawo sauyi da ta ƙunshi ginshiƙai shida, inda kiwon lafiya ya kasance ginshiƙi na uku, biyo bayan ilimi da tsaro.

“Manufarmu na farfaɗo da asibitoci shi ne mu tabbatar da cewa an samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga jama’ar mu, walau a yankunan karkara ko a birane. Wannan fahimtar ta sa muka gyara tare inganta cibiyoyin kiwon lafiya da suka lalace, musamman a garuruwa masu muhimmanci irin su Kaura Namoda, da ke a tsakanin ƙananan hukumomi da kuma zama wuri mafi sauƙi ga yankunan da ke kewaye.

“Na yi farin cikin bayar da rahoton cewa, a cikin watanni 14 da suka gabata, mun samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari wajen gyara da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar nan.

gwamna

“Har ila yau, mun kammala shirye-shiryen ɗaukar ma’aikatan kiwon lafiya da horar da su, sayen magunguna da kayan aiki masu muhimmanci, da gabatar da ayyukan kula da lafiyar mata da yara kyauta.

“Muna fatan waɗannan ayyukan za su haifar da ingantacciyar lafiya ga jama’armu ta hanyar rage mace-macen mata masu juna biyu, mace-macen jarirai, da daƙile cututtuka a faɗin jihar.

  • Badakalar Kudade: Kotun Daukaka Kara Ta Nemi Tsohon Gwamnan Kogi Ya Gurfanar Da Kansa A Kotu

 

“Bikin ƙaddamarwar na yau ya nuna aniyarmu ta samar da ingantaccen kiwon lafiya ga ɗaukacin mazauna Zamfara, ba tare da la’akari da wurinsu, matsayinsu ko kuɗin da suke samu ba.

“Tsarin aikin ya haɗa da sake gyara asibitin gaba ɗaya, tare da samar da tsayayyen wutar lantarki mai ƙarfin 32 kW, da sanya fitulun titi 25, da kuma samar da muhimman kayan aiki ga likitoci. Bayan kammala wannan ginin cikin nasara, ina da yaƙinin cewa mutanen Kaura Namoda da garuruwa da ƙauyukan da ke maƙwabtaka da su, yanzu za su samu damar cin moriyar kiwon lafiya mai sauƙi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha
Kiwon Lafiya

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Kiwon Lafiya

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Next Post
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

An Kama Dan Uwan Kwankwaso Da Wasu 4 Kan Badakalar Magani A Kano

LABARAI MASU NASABA

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.