ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Asibitin Ƙauran Namoda Da Ya Inganta

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

A ranar Talatar nan ne Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda, wanda aka yi masa gyara, tare da wadata shi da kayan aikin kula da lafiya.

Babban asibitin, yana kula da Ƙauran Namoda da maƙwabtanta, wanda kuma aka wadata shi da kayan aiki don ya samar da iingantacen kiwon lafiya.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa babban asibitin, an samar masa da kayan aikin kula da lafiya, waɗanda suka haɗa da na’urorin binciken cututtuka, gadajen haihuwa, na’urar auna bugun zuciya (ECG), na’urorin binciken jini, babbar na’urar binciken jini ta ‘automatic hematology analyzer’, na’urar auna nauyi ta zamani, fitilar haskawa yayin aikin tiyata da dai wasu kayan kula da lafiya da daman gaske.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa, asibitocin gaba ɗaya na da matuƙar muhimmanci wajen samar da ingantaccen kiwon lafiya, wanda ya kamata ya zama mai sauƙi ga al’ummar Jihar Zamfara.

A wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya nanata cewa babban abin da gwamnatinsa ta mayar da hankali a kai shi ne farfaɗo da taɓarɓarewar ababen more rayuwa da magance matsalolin da ke addabar dukkanin sassan tattalin arzikin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

gwamna

“Wannan hangen nesa ya sa muka yanke shawarar samar da ajandar kawo sauyi da ta ƙunshi ginshiƙai shida, inda kiwon lafiya ya kasance ginshiƙi na uku, biyo bayan ilimi da tsaro.

“Manufarmu na farfaɗo da asibitoci shi ne mu tabbatar da cewa an samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga jama’ar mu, walau a yankunan karkara ko a birane. Wannan fahimtar ta sa muka gyara tare inganta cibiyoyin kiwon lafiya da suka lalace, musamman a garuruwa masu muhimmanci irin su Kaura Namoda, da ke a tsakanin ƙananan hukumomi da kuma zama wuri mafi sauƙi ga yankunan da ke kewaye.

“Na yi farin cikin bayar da rahoton cewa, a cikin watanni 14 da suka gabata, mun samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari wajen gyara da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar nan.

gwamna

“Har ila yau, mun kammala shirye-shiryen ɗaukar ma’aikatan kiwon lafiya da horar da su, sayen magunguna da kayan aiki masu muhimmanci, da gabatar da ayyukan kula da lafiyar mata da yara kyauta.

“Muna fatan waɗannan ayyukan za su haifar da ingantacciyar lafiya ga jama’armu ta hanyar rage mace-macen mata masu juna biyu, mace-macen jarirai, da daƙile cututtuka a faɗin jihar.

  • Badakalar Kudade: Kotun Daukaka Kara Ta Nemi Tsohon Gwamnan Kogi Ya Gurfanar Da Kansa A Kotu

 

“Bikin ƙaddamarwar na yau ya nuna aniyarmu ta samar da ingantaccen kiwon lafiya ga ɗaukacin mazauna Zamfara, ba tare da la’akari da wurinsu, matsayinsu ko kuɗin da suke samu ba.

“Tsarin aikin ya haɗa da sake gyara asibitin gaba ɗaya, tare da samar da tsayayyen wutar lantarki mai ƙarfin 32 kW, da sanya fitulun titi 25, da kuma samar da muhimman kayan aiki ga likitoci. Bayan kammala wannan ginin cikin nasara, ina da yaƙinin cewa mutanen Kaura Namoda da garuruwa da ƙauyukan da ke maƙwabtaka da su, yanzu za su samu damar cin moriyar kiwon lafiya mai sauƙi.”

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

An Kama Dan Uwan Kwankwaso Da Wasu 4 Kan Badakalar Magani A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.