• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hukumar Leken Asirin Burtaniya Ta Dakile Yunkurin Kisan Fafaroma

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
Fafaroma

Hukumar leken asirin Burtaniya ta dakile yunkurin kashe Fafaroma Francis a wani lokacin da ya kai wata ziyara Iraki.

Wannan labarin na cikin tsakuren littafin tarihin rayuwarsa da ake dako, inda a ciki ya rubuta cewa bayan ya isa birnin Baghdad a watan Maris na 2021 ne aka sanar da shi cewa taron da zai halarta, akwai masu harin kunar bakin wake guda biyu da suke tarwatsa mutane.

  • Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026
  • Kudirin Dokar Haramta Amfani Da Kudaden Waje Ya Tsallake Karatu Na Farko A Majalisa

Daga bisani an kama mutanen da suke shirin kai harin.

Ziyarar ce ta farko da wani fafaroma zai kai a kasar Iraki, wadda kuma ya yi a lokacin da ake tsaka da annobar Korona.

“Kusan duk wadanda na yi shawara da su, sai da suka nuna min rashin amincewarsu da ziyarar,” in ji shi, sannan ya kara da cewa shi kuma ya yi tunanin ziyara ce mai matukar muhimmanci.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jawabin Janar Tiani Ranar Cika Shekaru 66 Da Nijar Ta Zama Jamhuriya

Shugaban gwamnatin mulkin sojan Jamhuryar Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya yi jawabi ga al’umma ranar bikin samun ‘yancin kai inda ya tabo mahimman batutuwan da suka shafi tafiyar kasar daga lokacin da ya kwaci madafun iko zuwa yau.

A jawabin na mintocin kusan 30, shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar ya yi bitar nasarorin da aka samu daga darewar CNSP kan karaga kawo yau.

Ya ce ” Mun kori sojojin kasashen waje ba tare da nuna kyama ko wata rigima ba wadanda a baya suke yi wa ‘yancin kasarmu barazana suna kuma hana dakarunmu sukunin gudanar da aikinsu kamar yadda ya dace. Haka kuma, mun soke dukkan wasu kwangiloli da dukkan wasu dokoki da yarjeniyoyi na rashin adalci wadanda ba sa amfana wa Nijer komai, kuma su ke dakushe ci gabanta.

Sannan ya ce an yi nasara wajen hada kan al’umma a game da abin da ya shafi muradun kasa ma’ana, daga yanzu dukkan ‘yan Nijer alkibla daya suke kallo. A yau Nijer ta gwada cewa, za ta iya tsayuwa da kafafunta ta tunkari matsalolin ta’addanci ta kuma yi nasara, ta biya albashin ma’aikatanta ta kuma dauki dawainiyar bukatun kanta da kanta.

Janar Tiani ya ce, kasar za ta iya rayuwa ba tare da jiran tallafin da ake cewa tana samu daga waje ba wadanda wani bi ake fakewa da su don yi wa ‘yan Nijer barazana ko a wulakanta su.

Ya kuma bayyana cewa, “A karon farko a tarihin Nijer, dukkan wasu matakai da suka shafi kasar da ‘ya’yanta ana daukansu ne a nan gida daga ‘yan kasa domin amfanin Nijer, dalilin haka ne ma ya sa duk da mawuyacin halin da ake ciki aka dauki matakin samar da sassaucin rayuwa ga al’umma ta hanyar rage kudin man fetur da rage kudin likita da rage farashin siminti.”

Ya na mai alfahari da sabuwar alakar kasar da wasu kasashen waje.

A game da batun ficewa daga CEDEAO ya nanata cewa, ba makawa, kasashen nan 3 sun balle ba fashi domin kare ‘yancin kai da tabbatar da tsaro a yankin. Ya ce wanan kuma mataki ne da ke toshe dukkan hanyoyin da manyan kasashe ke bi su fake da CEDEAO su yaki kasashen AES.

Shugaban gwamnatin mulkin sojan, ya sake nanata alkawalin rike amanar da ya dauka, ya jinjina wa dakarun tsaro saboda jajircewarsu akan tsaron kasa a wannan lokaci na gwabza yaki da ‘yan ta’adda, haka kuma ya yaba wa al’ummar kasar sabili da yadda suke ci gaba da nuna juriya kan mawuyacin halin da ake ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 
Labarai

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba
Labarai

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Next Post
katsina

Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.