ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hukumar Leken Asirin Burtaniya Ta Dakile Yunkurin Kisan Fafaroma

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
11 months ago
Fafaroma

Hukumar leken asirin Burtaniya ta dakile yunkurin kashe Fafaroma Francis a wani lokacin da ya kai wata ziyara Iraki.

Wannan labarin na cikin tsakuren littafin tarihin rayuwarsa da ake dako, inda a ciki ya rubuta cewa bayan ya isa birnin Baghdad a watan Maris na 2021 ne aka sanar da shi cewa taron da zai halarta, akwai masu harin kunar bakin wake guda biyu da suke tarwatsa mutane.

  • Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026
  • Kudirin Dokar Haramta Amfani Da Kudaden Waje Ya Tsallake Karatu Na Farko A Majalisa

Daga bisani an kama mutanen da suke shirin kai harin.

ADVERTISEMENT

Ziyarar ce ta farko da wani fafaroma zai kai a kasar Iraki, wadda kuma ya yi a lokacin da ake tsaka da annobar Korona.

“Kusan duk wadanda na yi shawara da su, sai da suka nuna min rashin amincewarsu da ziyarar,” in ji shi, sannan ya kara da cewa shi kuma ya yi tunanin ziyara ce mai matukar muhimmanci.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Jawabin Janar Tiani Ranar Cika Shekaru 66 Da Nijar Ta Zama Jamhuriya

Shugaban gwamnatin mulkin sojan Jamhuryar Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya yi jawabi ga al’umma ranar bikin samun ‘yancin kai inda ya tabo mahimman batutuwan da suka shafi tafiyar kasar daga lokacin da ya kwaci madafun iko zuwa yau.

A jawabin na mintocin kusan 30, shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar ya yi bitar nasarorin da aka samu daga darewar CNSP kan karaga kawo yau.

Ya ce ” Mun kori sojojin kasashen waje ba tare da nuna kyama ko wata rigima ba wadanda a baya suke yi wa ‘yancin kasarmu barazana suna kuma hana dakarunmu sukunin gudanar da aikinsu kamar yadda ya dace. Haka kuma, mun soke dukkan wasu kwangiloli da dukkan wasu dokoki da yarjeniyoyi na rashin adalci wadanda ba sa amfana wa Nijer komai, kuma su ke dakushe ci gabanta.

Sannan ya ce an yi nasara wajen hada kan al’umma a game da abin da ya shafi muradun kasa ma’ana, daga yanzu dukkan ‘yan Nijer alkibla daya suke kallo. A yau Nijer ta gwada cewa, za ta iya tsayuwa da kafafunta ta tunkari matsalolin ta’addanci ta kuma yi nasara, ta biya albashin ma’aikatanta ta kuma dauki dawainiyar bukatun kanta da kanta.

Janar Tiani ya ce, kasar za ta iya rayuwa ba tare da jiran tallafin da ake cewa tana samu daga waje ba wadanda wani bi ake fakewa da su don yi wa ‘yan Nijer barazana ko a wulakanta su.

Ya kuma bayyana cewa, “A karon farko a tarihin Nijer, dukkan wasu matakai da suka shafi kasar da ‘ya’yanta ana daukansu ne a nan gida daga ‘yan kasa domin amfanin Nijer, dalilin haka ne ma ya sa duk da mawuyacin halin da ake ciki aka dauki matakin samar da sassaucin rayuwa ga al’umma ta hanyar rage kudin man fetur da rage kudin likita da rage farashin siminti.”

Ya na mai alfahari da sabuwar alakar kasar da wasu kasashen waje.

A game da batun ficewa daga CEDEAO ya nanata cewa, ba makawa, kasashen nan 3 sun balle ba fashi domin kare ‘yancin kai da tabbatar da tsaro a yankin. Ya ce wanan kuma mataki ne da ke toshe dukkan hanyoyin da manyan kasashe ke bi su fake da CEDEAO su yaki kasashen AES.

Shugaban gwamnatin mulkin sojan, ya sake nanata alkawalin rike amanar da ya dauka, ya jinjina wa dakarun tsaro saboda jajircewarsu akan tsaron kasa a wannan lokaci na gwabza yaki da ‘yan ta’adda, haka kuma ya yaba wa al’ummar kasar sabili da yadda suke ci gaba da nuna juriya kan mawuyacin halin da ake ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
katsina

Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.