• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hukumar Leken Asirin Burtaniya Ta Dakile Yunkurin Kisan Fafaroma

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Yadda Hukumar Leken Asirin Burtaniya Ta Dakile Yunkurin Kisan Fafaroma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar leken asirin Burtaniya ta dakile yunkurin kashe Fafaroma Francis a wani lokacin da ya kai wata ziyara Iraki.

Wannan labarin na cikin tsakuren littafin tarihin rayuwarsa da ake dako, inda a ciki ya rubuta cewa bayan ya isa birnin Baghdad a watan Maris na 2021 ne aka sanar da shi cewa taron da zai halarta, akwai masu harin kunar bakin wake guda biyu da suke tarwatsa mutane.

  • Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026
  • Kudirin Dokar Haramta Amfani Da Kudaden Waje Ya Tsallake Karatu Na Farko A Majalisa

Daga bisani an kama mutanen da suke shirin kai harin.

Ziyarar ce ta farko da wani fafaroma zai kai a kasar Iraki, wadda kuma ya yi a lokacin da ake tsaka da annobar Korona.

“Kusan duk wadanda na yi shawara da su, sai da suka nuna min rashin amincewarsu da ziyarar,” in ji shi, sannan ya kara da cewa shi kuma ya yi tunanin ziyara ce mai matukar muhimmanci.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Jawabin Janar Tiani Ranar Cika Shekaru 66 Da Nijar Ta Zama Jamhuriya

Shugaban gwamnatin mulkin sojan Jamhuryar Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya yi jawabi ga al’umma ranar bikin samun ‘yancin kai inda ya tabo mahimman batutuwan da suka shafi tafiyar kasar daga lokacin da ya kwaci madafun iko zuwa yau.

A jawabin na mintocin kusan 30, shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar ya yi bitar nasarorin da aka samu daga darewar CNSP kan karaga kawo yau.

Ya ce ” Mun kori sojojin kasashen waje ba tare da nuna kyama ko wata rigima ba wadanda a baya suke yi wa ‘yancin kasarmu barazana suna kuma hana dakarunmu sukunin gudanar da aikinsu kamar yadda ya dace. Haka kuma, mun soke dukkan wasu kwangiloli da dukkan wasu dokoki da yarjeniyoyi na rashin adalci wadanda ba sa amfana wa Nijer komai, kuma su ke dakushe ci gabanta.

Sannan ya ce an yi nasara wajen hada kan al’umma a game da abin da ya shafi muradun kasa ma’ana, daga yanzu dukkan ‘yan Nijer alkibla daya suke kallo. A yau Nijer ta gwada cewa, za ta iya tsayuwa da kafafunta ta tunkari matsalolin ta’addanci ta kuma yi nasara, ta biya albashin ma’aikatanta ta kuma dauki dawainiyar bukatun kanta da kanta.

Janar Tiani ya ce, kasar za ta iya rayuwa ba tare da jiran tallafin da ake cewa tana samu daga waje ba wadanda wani bi ake fakewa da su don yi wa ‘yan Nijer barazana ko a wulakanta su.

Ya kuma bayyana cewa, “A karon farko a tarihin Nijer, dukkan wasu matakai da suka shafi kasar da ‘ya’yanta ana daukansu ne a nan gida daga ‘yan kasa domin amfanin Nijer, dalilin haka ne ma ya sa duk da mawuyacin halin da ake ciki aka dauki matakin samar da sassaucin rayuwa ga al’umma ta hanyar rage kudin man fetur da rage kudin likita da rage farashin siminti.”

Ya na mai alfahari da sabuwar alakar kasar da wasu kasashen waje.

A game da batun ficewa daga CEDEAO ya nanata cewa, ba makawa, kasashen nan 3 sun balle ba fashi domin kare ‘yancin kai da tabbatar da tsaro a yankin. Ya ce wanan kuma mataki ne da ke toshe dukkan hanyoyin da manyan kasashe ke bi su fake da CEDEAO su yaki kasashen AES.

Shugaban gwamnatin mulkin sojan, ya sake nanata alkawalin rike amanar da ya dauka, ya jinjina wa dakarun tsaro saboda jajircewarsu akan tsaron kasa a wannan lokaci na gwabza yaki da ‘yan ta’adda, haka kuma ya yaba wa al’ummar kasar sabili da yadda suke ci gaba da nuna juriya kan mawuyacin halin da ake ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Next Post

Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

Related

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

7 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

7 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

8 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

9 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

10 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

12 hours ago
Next Post
katsina

Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Dakile Rikici Tsakanin Makiyaya Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.