• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
6 months ago
in Manyan Labarai
0
Zargin Yaudara: Wani Tela Ya Kashe Tsohuwar Masoyiyarsa A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Sana’ar Na Karfafa Ayyukan Bata-gari –Hukuma
  • Wannan Shirin Zai Tsaftace Sana’armu –Shugaban Kungiyar

Hukumomin tsaro a Babban Birnin Tarayya Abuja sun fara farautar ‘yan kasuwar Jari Bola (dillalan shara).

Ko’odinetan Hukumar Kula Da Harkokin Birnin Tarayya Abuja (AMMC), Cif Felid Obuah, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da jami’an kasuwar fanteka a Abuja.

  • Sam Ba Ni Da Labari Kan Abin Da Ya Faru A Unguwar Rimin Zakara – Abba Gida-Gida
  • Zanga-zanga: Ku Kawo Ƙarshen Rashin Wutar Lantarki Da Ta Addabi Jihohi- Gwamnatin Kaduna 

Obuah ya bayyana cewa an fara wannan shiri ne don inganta sa ido da ka’idojin ayyuka a duk kasuwannin pantaker da ke fadin FCT.

A cewarsa, aikin ya biyo bayan matakin da kwamitin tsaro na Babban Birnin Tarayya Abuja ya dauka ne a ranar 13 ga watan Janairu na dakatar da ayyukan duk kasuwannin Jari Bola na tsawon makwanni biyu.

“Kalmar ‘pantaker’ tana nufin kasuwannin da suka kware wajen sayar da kayayyaki na hannu da kayan tarkace, gami da kayan daki da kayan gida,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Obuah ya ce, makasudin yin bayanin shi ne don tabbatar da cewa masu aiki da doka ne kawai ke aiki a Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma yaki da matsalar masu barna a yankin.

Ya ci gaba da cewa, wani samame da ‘yansanda suka kai a wasu kasuwannin Pantaker a baya-bayan nan ya yi nasarar kwato dukiyar al’umma da aka sace da suka kai sama da Naira biliyan daya.

“Saboda haka, Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja, tare da jami’an tsaro, ta bayar da umarnin cewa duk wani ma’aikacin pantaker dole ne a yi rajista da kuma bayyana sunansa. Wannan zai ba mu damar gano masu aiki na gaske kuma mu fahimci ayyukan kasuwancinsu.

“Haka zalika za a bukaci masu gudanar da aikin su rike rajistar masu saye da masu kaya. Muna bukatar mu san su wanene masu samar muku da kaya kuma wa kuke sayarwa. Samun wannan bayanin zai taimaka a kokarinmu na tsaro,” Obuah ya kara da cewa.

Ya shawarci masu sana’ar pantaker da su guji yin mu’amala da wasu mutane ba bisa ka’ida ba ko sayen kayan sata, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da irin wannan kayan zai fuskanci kamawa tare da gurfanar da shi gaban kuliya.

Obuah ya kuma kara karfafa gwiwar ma’aikatan da su hada kai a karkashin wata kungiya domin samar da ingantaccen hadin gwiwa da gwamnati da hukumomin tsaro.

Daraktan Sashen Tsaro na Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja, Adamu Gwary, ya jaddada cewa masu sana’ar sayar Jari Bola ne kawai da aka sani za a yi musu bayani kuma a ba su izinin sake bude kasuwancinsu.

Ya umurci duk ma’aikatan da ba su yi rijista ba da su bi tsarin tantancewa kafin su ci gaba da aiki.

Da yake mayar da martani, Shugaban Masu Sana’ar Pantaker Operators na Kasa, Alhaji Abbas Bello, ya bayyana kudirin ma’aikatan na tallafa wa kokarin da suke yi na inganta sana’o’insu.

Ya yarda cewa akwai masu aikata laifuka a cikinsu kuma ya yi maraba da shirin a matsayin hanyar kawar da su.

Sakataren Kungiyar Malam Salisu Abubakar ya tabbatar da shirinsu na hada kai da jami’an tsaro domin yakar wannan barna a Babban Birnin Tarayya Abuja


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Amince Da Yi Wa Masu Daukar Nauyin Ta’addanci Shari’a A Sirrance Ba

Next Post

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

14 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

20 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.