ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan

by Bello Hamza
1 year ago
Naira

Janye tallafi man fetur da aka yi a kwanan nan da kuma karya darajar naira sun shafi manya da kananan masana’atu da dama a Nijeriya, wanda hakan ya kai ga raguwar kudaden shiga da kuma matsalolin da suka shafi kudade gudanarwa.

Tunda aka janye tallafin mai a ranar 29 ga watan Mayu a shekarar 2023, farashin man fetur ta tashi kashi fiye da 193 abin da ya hargitsa tare da haifar da rudani a bangaren.

  • Sin Ta Kulla Yarjejeniyar Tsarin Kafa Huldar Abota Ta Raya Tattalin Arziki Cikin Hadin Gwiwa Tsakaninta Da Kasashen Afirka 22.
  • Hukumar Zaɓe Ta Jihar Kano Ta Rage Farashin Takardar Tsayawa t Takara

Lamarin ya fi shafar masu masana’antu ne saboda karuwar farashi man fetur da karuwar farashi kayan da ake sarrafawa ya haifar da tsadar kayan aiki gaba daya.

ADVERTISEMENT

Rahaoto ya nuna cewa, kudaden haraji daga bangaren masana’antu ya yi kasa da fiye da kashi 70 a zangon farko na shekarar 2024, wanda ke nuna irin matsalar da bangaren masana’antun ke fuskanta.

Haka kuma karyewar darajar naira ya sanya shigo da yayakin daga kasashen waje ya kara tsada, abin da ya kara hauhawar farashi da nakasa abin da yake hannun masu saye da sayarwa.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Wannan ya kuma rage bukatar da al’umma ke yi wa kayyakin da aka sarrafa a masana’antu, hakan ya kuma kara karya bangare gaba daya. Masu fashin baki sun bayyana cewa, wadanan tsare-tsaren tattalin arzikin, wanda zai hana masu masana’antu samun riba a harkokinsu.

Ana matukar sukar gwamnatin Nijeriya a kan yadda ta aiwatar da wadannan tsare- tsaren ba tare da cikakken tattaunawa tare da nema jin ra’ayin al’umma ba, ba kuma tare da ta samar da wasu hayoyin rage wa masu masana’antu radadin da za su shiga ba sakamakon wadannan tsare-tsare na gwamnati ba, haka ya sa ake ganin rashin kwarewar mukarraban gwamanatin da kuma kwarwarsu a bangaren farfado da tattalin arziki.

A tsokacinsa, shugaban kamfanin Coleman Wires and Cables Industries Limited, George Onafowokan, ya kwatanta shekarar 2024 a matsayin shekarar da ba ta yi wa masu masaa’antu dadi ba, ya bayar da misali karyewar darajar naira, jaye tallafin mai da kuma rashin tabbas a bangare tattali arzikin kasa a mastayin matsaloli da za su ci gaba da cutar da masana’atu a kasar nan.

A tattaunawar da aka yi da shi, ya ce, wadannan tsare-tsare sun yi matukar shafar bangaren masu masana’antu a sassan Nijeriya tun a watan Mayu na shekarar 2023, ya ce, zuwa yanzu ana ci gaba da karya darajar Naira, yayin da janye talafin mai ya haifar da karuwar kudin sufuri ya kuma shafi dukkan bangarorin tattalin arzikin kasa.

A cewarsa babu wani da bai dandana sakamakon matsalar tattalin arzikin nan ba domin shekarar gaba daya ta zo a hagunce ga dukkan bangarorin tattalin arziki Nijeriya musamman bangaren masana’antu.

“Ci gaban harkokin kasuwanci a yau na bukatar jajircewa mai yawa saboda rashin tabbas a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji Onafowokan, ya kuma ce, rashin tabbas a farashin naira ya sa ba zai yiwu mutum ya yi tsare-tsare da hasashen ko kuma tsara harkokin kaswuancinsa ba.

Ya kuma karfafa masu masaa’antua kan karfafa fata dukda mastralo,I da ake fuskanta, y ace, in har aka ki karfafa fata to daga karshe za a kai ga rufe masana’antun ke nan.

Onafowokan ya kuma ce, ya kamata gwamnati ta bayar da umarni samar da bashi ga ,masu masana’antu ta hanyar Bakin Masana’anatu, ya ce wanann mataki ne da zai farfado da masana’antu da dama a fadin kasar nan.

Ya kuma nemi a rage wa masu masaa’atu harajin da suke biya akan kayan da suke shigo da shi wadanda suke sarrafawa don tabbbatar da masana’antu na ci ga da rayuwa duk da matsalar tattali arzikj da ake fuskanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Tattalin Arziki

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma'adanai Don Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

November 11, 2025
APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.