• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan

by Bello Hamza
8 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Janye tallafi man fetur da aka yi a kwanan nan da kuma karya darajar naira sun shafi manya da kananan masana’atu da dama a Nijeriya, wanda hakan ya kai ga raguwar kudaden shiga da kuma matsalolin da suka shafi kudade gudanarwa.

Tunda aka janye tallafin mai a ranar 29 ga watan Mayu a shekarar 2023, farashin man fetur ta tashi kashi fiye da 193 abin da ya hargitsa tare da haifar da rudani a bangaren.

  • Sin Ta Kulla Yarjejeniyar Tsarin Kafa Huldar Abota Ta Raya Tattalin Arziki Cikin Hadin Gwiwa Tsakaninta Da Kasashen Afirka 22.
  • Hukumar Zaɓe Ta Jihar Kano Ta Rage Farashin Takardar Tsayawa t Takara

Lamarin ya fi shafar masu masana’antu ne saboda karuwar farashi man fetur da karuwar farashi kayan da ake sarrafawa ya haifar da tsadar kayan aiki gaba daya.

Rahaoto ya nuna cewa, kudaden haraji daga bangaren masana’antu ya yi kasa da fiye da kashi 70 a zangon farko na shekarar 2024, wanda ke nuna irin matsalar da bangaren masana’antun ke fuskanta.

Haka kuma karyewar darajar naira ya sanya shigo da yayakin daga kasashen waje ya kara tsada, abin da ya kara hauhawar farashi da nakasa abin da yake hannun masu saye da sayarwa.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Wannan ya kuma rage bukatar da al’umma ke yi wa kayyakin da aka sarrafa a masana’antu, hakan ya kuma kara karya bangare gaba daya. Masu fashin baki sun bayyana cewa, wadanan tsare-tsaren tattalin arzikin, wanda zai hana masu masana’antu samun riba a harkokinsu.

Ana matukar sukar gwamnatin Nijeriya a kan yadda ta aiwatar da wadannan tsare- tsaren ba tare da cikakken tattaunawa tare da nema jin ra’ayin al’umma ba, ba kuma tare da ta samar da wasu hayoyin rage wa masu masana’antu radadin da za su shiga ba sakamakon wadannan tsare-tsare na gwamnati ba, haka ya sa ake ganin rashin kwarewar mukarraban gwamanatin da kuma kwarwarsu a bangaren farfado da tattalin arziki.

A tsokacinsa, shugaban kamfanin Coleman Wires and Cables Industries Limited, George Onafowokan, ya kwatanta shekarar 2024 a matsayin shekarar da ba ta yi wa masu masaa’antu dadi ba, ya bayar da misali karyewar darajar naira, jaye tallafin mai da kuma rashin tabbas a bangare tattali arzikin kasa a mastayin matsaloli da za su ci gaba da cutar da masana’atu a kasar nan.

A tattaunawar da aka yi da shi, ya ce, wadannan tsare-tsare sun yi matukar shafar bangaren masu masana’antu a sassan Nijeriya tun a watan Mayu na shekarar 2023, ya ce, zuwa yanzu ana ci gaba da karya darajar Naira, yayin da janye talafin mai ya haifar da karuwar kudin sufuri ya kuma shafi dukkan bangarorin tattalin arzikin kasa.

A cewarsa babu wani da bai dandana sakamakon matsalar tattalin arzikin nan ba domin shekarar gaba daya ta zo a hagunce ga dukkan bangarorin tattalin arziki Nijeriya musamman bangaren masana’antu.

“Ci gaban harkokin kasuwanci a yau na bukatar jajircewa mai yawa saboda rashin tabbas a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji Onafowokan, ya kuma ce, rashin tabbas a farashin naira ya sa ba zai yiwu mutum ya yi tsare-tsare da hasashen ko kuma tsara harkokin kaswuancinsa ba.

Ya kuma karfafa masu masaa’antua kan karfafa fata dukda mastralo,I da ake fuskanta, y ace, in har aka ki karfafa fata to daga karshe za a kai ga rufe masana’antun ke nan.

Onafowokan ya kuma ce, ya kamata gwamnati ta bayar da umarni samar da bashi ga ,masu masana’antu ta hanyar Bakin Masana’anatu, ya ce wanann mataki ne da zai farfado da masana’antu da dama a fadin kasar nan.

Ya kuma nemi a rage wa masu masaa’atu harajin da suke biya akan kayan da suke shigo da shi wadanda suke sarrafawa don tabbbatar da masana’antu na ci ga da rayuwa duk da matsalar tattali arzikj da ake fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DarajaKaryewaNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

6 days ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

6 days ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

2 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

3 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

3 weeks ago
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma'adanai Don Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.