• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan

by Bello Hamza
10 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Janye tallafi man fetur da aka yi a kwanan nan da kuma karya darajar naira sun shafi manya da kananan masana’atu da dama a Nijeriya, wanda hakan ya kai ga raguwar kudaden shiga da kuma matsalolin da suka shafi kudade gudanarwa.

Tunda aka janye tallafin mai a ranar 29 ga watan Mayu a shekarar 2023, farashin man fetur ta tashi kashi fiye da 193 abin da ya hargitsa tare da haifar da rudani a bangaren.

  • Sin Ta Kulla Yarjejeniyar Tsarin Kafa Huldar Abota Ta Raya Tattalin Arziki Cikin Hadin Gwiwa Tsakaninta Da Kasashen Afirka 22.
  • Hukumar Zaɓe Ta Jihar Kano Ta Rage Farashin Takardar Tsayawa t Takara

Lamarin ya fi shafar masu masana’antu ne saboda karuwar farashi man fetur da karuwar farashi kayan da ake sarrafawa ya haifar da tsadar kayan aiki gaba daya.

Rahaoto ya nuna cewa, kudaden haraji daga bangaren masana’antu ya yi kasa da fiye da kashi 70 a zangon farko na shekarar 2024, wanda ke nuna irin matsalar da bangaren masana’antun ke fuskanta.

Haka kuma karyewar darajar naira ya sanya shigo da yayakin daga kasashen waje ya kara tsada, abin da ya kara hauhawar farashi da nakasa abin da yake hannun masu saye da sayarwa.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Wannan ya kuma rage bukatar da al’umma ke yi wa kayyakin da aka sarrafa a masana’antu, hakan ya kuma kara karya bangare gaba daya. Masu fashin baki sun bayyana cewa, wadanan tsare-tsaren tattalin arzikin, wanda zai hana masu masana’antu samun riba a harkokinsu.

Ana matukar sukar gwamnatin Nijeriya a kan yadda ta aiwatar da wadannan tsare- tsaren ba tare da cikakken tattaunawa tare da nema jin ra’ayin al’umma ba, ba kuma tare da ta samar da wasu hayoyin rage wa masu masana’antu radadin da za su shiga ba sakamakon wadannan tsare-tsare na gwamnati ba, haka ya sa ake ganin rashin kwarewar mukarraban gwamanatin da kuma kwarwarsu a bangaren farfado da tattalin arziki.

A tsokacinsa, shugaban kamfanin Coleman Wires and Cables Industries Limited, George Onafowokan, ya kwatanta shekarar 2024 a matsayin shekarar da ba ta yi wa masu masaa’antu dadi ba, ya bayar da misali karyewar darajar naira, jaye tallafin mai da kuma rashin tabbas a bangare tattali arzikin kasa a mastayin matsaloli da za su ci gaba da cutar da masana’atu a kasar nan.

A tattaunawar da aka yi da shi, ya ce, wadannan tsare-tsare sun yi matukar shafar bangaren masu masana’antu a sassan Nijeriya tun a watan Mayu na shekarar 2023, ya ce, zuwa yanzu ana ci gaba da karya darajar Naira, yayin da janye talafin mai ya haifar da karuwar kudin sufuri ya kuma shafi dukkan bangarorin tattalin arzikin kasa.

A cewarsa babu wani da bai dandana sakamakon matsalar tattalin arzikin nan ba domin shekarar gaba daya ta zo a hagunce ga dukkan bangarorin tattalin arziki Nijeriya musamman bangaren masana’antu.

“Ci gaban harkokin kasuwanci a yau na bukatar jajircewa mai yawa saboda rashin tabbas a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji Onafowokan, ya kuma ce, rashin tabbas a farashin naira ya sa ba zai yiwu mutum ya yi tsare-tsare da hasashen ko kuma tsara harkokin kaswuancinsa ba.

Ya kuma karfafa masu masaa’antua kan karfafa fata dukda mastralo,I da ake fuskanta, y ace, in har aka ki karfafa fata to daga karshe za a kai ga rufe masana’antun ke nan.

Onafowokan ya kuma ce, ya kamata gwamnati ta bayar da umarni samar da bashi ga ,masu masana’antu ta hanyar Bakin Masana’anatu, ya ce wanann mataki ne da zai farfado da masana’antu da dama a fadin kasar nan.

Ya kuma nemi a rage wa masu masaa’atu harajin da suke biya akan kayan da suke shigo da shi wadanda suke sarrafawa don tabbbatar da masana’antu na ci ga da rayuwa duk da matsalar tattali arzikj da ake fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DarajaKaryewaNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

Related

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

3 days ago
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

3 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 month ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma'adanai Don Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.