• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Bai Wa Kowane Bangare Hakkinsa Daga Jawaban Shugaba Xi

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Sin

Sau da yawa mutane kan yi mamakin irin hikimomin kasar Sin mai al’umma kusan biliyan daya da rabi ke amfani da su, wajen gudanar da al’amuranta, saboda yadda wasu ke cewa “idan dambu ya yi yawa, ba ya jin mai”.

 

Bari mu zakulo wasu daga cikin hikimomin da kasar ke amfani da su daga jawaban da Shugaba Xi Jinping ya gabatar a wurare da lokuta daban-daban.

  • Sarki Sanusi II Zai Sake Ayyana Wata Rana Ta Naɗa Sabon Hakimin Bichi
  • Kwamitin Ɗanyen Mai Ya Nuna Rashin Gamsuwa Da Jinkirin Haƙo Mai A Kolmani

Ga misalin farko game da nuna tausayin al’ummarta da kula da halin da jama’a za su shiga a kowane irin mataki da gwamnatin kasar za ta dauka.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

A taron tattaunawar da aka yi da wakilan ’yan kasuwa da masana ilimi a ranar 23 ga Mayun 2024, Shugaba Xi ya ce, “Kamata ya yi a dauki matakan gyare-gyaren da za su magance matsalolin da suka fi damun al’umma da kuma saurare da aiwatar da abin da suke so, sannan a dauki kwararan matakai da za su samar da fa’ida ta hakika ga jama’a, da samun amincewarsu da mutunta ra’ayoyinsu gwargwadon iko, ta yadda gyare-gyaren da ake yi za su tabbatar da cikar burinsu da faranta musu rai da ba su cikakken tsaro.”

 

Ina da yakinin duk wanda ya sa kafa a kasar Sin, zai ga abubuwan da shugaban ya ambata a aikace.

 

Har ila yau, a dai wannan taron da wakilan ’yan kasuwa da masana ilimi, shugaban ya ce, “Yana da matukar muhimmanci a bi abubuwa sau da kafa da kuma inganta tsarin tattalin arzikin kasarmu, da gina babban tsari na tafiyar da tattalin arzikin kasuwanci bisa turbar gurguzu, da inganta tsarin kula da kananan sana’o’i da hanyoyin samar da ci gaba mai inganci.”

 

A nan, za a fahimci irin yadda kasar Sin take bin tsare-tsaren kawo ci gaba,da kyautata yanayin kasuwanci, da nuna ishara ga masana ilimi a kan ba da gudummawa wajen bayar da shawarwari a kan kula da kananan sana’o’i, da kawo hanyoyin samar da ci gaba mai inganci.

 

Kamar an tambayi Shugaba Xi, to ta yaya kasar Sin take aiwatar da tsare-tsarenta cikin nasara? A jawabin da ya gabatar a zaman nazari na rukuni-rukuni da aka yi lokacin taron sashin siyasa na Kwamitin Tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis karo na 14, a ranar 27 ga Mayun 2024, ya ce, “Don magance matsalolin da suka shafi tsarin ayyukan yi da kawo ma’aikatan da ake bukatar a samar daidai da bukatu, ya kamata a yi kokarin hanzarta habaka samar da ma’aikata na zamani masu kwarewa da suka dace da zamani wadanda za su wadatar da kuma rarraba su a bisa ingantaccen tsari.”

 

Dangane da batun kimiyya da fasaha wanda duniya ke yi a zamanin nan, kasar Sin ta kasance jagora. Ga kuma daya daga cikin sirrukan kasar daga abin da Shugaba Xi ya ce a jawabinsa lokacin taron koli na kasa a kan kimiyya da fasaha da aka yi ranar 24 ga Yunin 2024, “Yana da matukar alfanu a sada tsakanin sabbin kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha da kuma ci gaban masana’antu, ta yadda hakan zai taimaka wajen samar da sabbin ginshakai na kawo ci gaba.”

 

A bangaren muhalli kuwa, a halin yanzu kowa ya san yadda ake tataburza a tsakanin kasashe masu tasowa da masu karfin tattalin arziki game da gurbata muhalli, ta wannan fuskar ma, kasar Sin tana ci gaba da daukar matakai a cikin gida da yekuwar hakan a waje. Shugaba Xi ya bayyana hikimar kasar Sin a taron koli na kasar a kan kiyaye lafiyar muhalli, da ya gudana ranar 19 ga Yunin 2023, inda ya ce, “Ya kamata babban matakin kare muhalli da ake dauka ya taimaka wa kasar Sin ta ci gaba da samar da sabbin turaku da hanyoyin raya kasa, da kara himma ga gina tattalin arziki mara gurbata muhalli. Ta haka kasar za ta yi tsimin kudin da take yawan kashewa da rage gurbata muhalli yadda ya kamata, sannan za ta ci gaba da karfafa kokarinta na dorad da ci gaba.”

 

Daga wadannan misalai daga jawaban Shugaba Xi, ana iya fahimtar yadda kasar Sin ke bai wa ko wane bangare hakkinsa domin samun dorewar ci gaba, ba kawai ga kanta ba har ma da duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Ɗangote Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasar Kamaru

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.