• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, an gudanar da taron kasa da kasa kan makamashi karo na 26 a birnin Rotterdam na kasar Netherlands. Taken taron shi ne “A sake tsara fasalin makamashi ga dan Adam da duniya”, a daidai lokacin da duniya ke fuskantar kalubale na sake fasalin makamashin da ake amfani da su, taron ya jawo wakilai kusan dubu 20 daga sassan makamashi na duniya. Amin Nasser, babban darektan kamfanin Saudi Aramco mai samar da man fetur na kasar Saudiyya, ya yaba da gudummawar da kasar Sin ta samar ta fannin cimma burin samun daidaito tsakanin yawan hayaki mai dumama yanayi da za a fitar, da yawan abubuwan da za su shawo kan hayakin a fadin duniya. A cewarsa, ta hanyar rage kudin sarrafa farantan samar da wutar lantarki ta hasken rana, kasar Sin ta tallafa wa kasashen duniya, ciki har da kasashen yamma, wajen bunkasa sabbin makamashi, kuma abin haka yake ta fannin motoci masu aiki da lantarki. 

A lokacin da kasar Amurka ke ta zargin kasar Sin da cewa wai “ta wuce misali wajen samar da sabbin makamashi”, furucin na malam Amin Nasser ya jawo hankalin kasa da kasa, ba kawai sabo da matsayinsa da na kamfaninsa ta fannin makamashin duniya ba, har da ma adalci da ya yi kan rawar da kasar Sin ke takawa wajen samar da makamashi mai tsabta, da ma rage fitar da iskar Carbon.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Faransa Da Serbiya Gami Da Hungary
  • CMG Ya Gudanar Da Bikin Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Yayata Tasharsa Ta 8K UHD

A halin da ake ciki na kara samun zafin yanayi, da ma bala’u daga indallahi, yana ta kara zama dole a sake fasalin makamashi da ake amfani da su. Duk da haka, aikin ba shi da sauki. Don tabbatar da daidaiton kasa da kasa na tinkarar sauyin yanayin duniya, a cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta dogara ga kirkire-kirkiren fasahohi, da manyan kasuwanninta, da cikakken tsarin masana’antunta, kuma ta yi ta samun ci gaba ta fannin sabbin makamashi. Ban da biyan bukatun cikin gida, kayayyaki masu nasaba da sabbin makamashi da kasar Sin ta samar sun kuma samar da dama ga kasashen duniya, musamman ma kasashen Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa, wajen sauya makamashin da suke amfani da su da ma tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

In mun duba kasashen Afirka, bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, kasar Sin ta aiwatar da shirye-shirye daruruwa na samar da wutar lantarki ta makamashi masu tsabta. A kasar Kenya, tashar samar da wutar lantarki da makamashin rana ta Garissa, wadda wani kamfanin kasar Sin ne ya gina, ta kasance mafi girma a gabashin Afirka, kuma bayan da aka fara aiki da ita a shekarar 2019, ta rika samar da wuta sama da KW miliyan 76 a kowace shekara, wadda ke iya biyan bukatun mutane sama da dubu 380, kana ta yi matukar saukaka matsalar karancin wutar lantarki da aka fuskanta a wurin. Sai kuma a Nijeriya, a watan Mayun bara, an fara aiki da bas-bas masu aiki da lantarki da kamfanin samar da bas-bas na kasar Sin ya samar, matakin da ke da matukar ma’ana ga tabbatar da dauwamammen ci gaban harkokin zirga-zirga, da ma sake fasalin makamashi a kasar da ma shiyyar yammacin Afirka baki daya. A ganin Adhere Cavince, masanin ilmin huldar kasa da kasa na kasar Kenya, kasar Sin ba kawai tana kokarin sauya makamashin da take amfani da su ba, har kullum tana kuma hada kai da kasashen Afirka, har ma ta zama babbar abokiyar hadin gwiwa ga kasashen Afirka, wajen bunkasa makamashin da ake samarwa ta hasken rana da kuma karfin iska.

Ya zuwa bara, shekaru 10 a jere ke nan kasar Sin tana kan matsayi na farko a duniya, wajen samar da wutar lantarki da sabbin makamashi. Ban da haka, kasar Sin ta kuma samar da kaso 50% na na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska, da kuma kaso 80% na na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana da ake bukata a duniya. A cikin shekaru 10 da suka wuce, matsakaicin kudin da ake bukata wajen samar da wutar lantarki ta karfin iska da ta hasken rana, ya ragu da kashi 60% da kuma 80% kowanensu, kuma hakan ba ya rasa nasaba da babbar gudummawar da kasar Sin ta bayar. A wata makala da kafar Bloomburg ta fitar, an ce, kayayyaki masu nasaba da sabbin makamashi da kasar Sin ta samar cikin farashi mai sauki, sun samar da damar sauya fasalin makamashin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Amma duk da haka, ko ta fannin cimma burin da aka saka a yarjejeniyar Paris, ko kuma ta cimma burin kasar Sin na kaiwa kololuwar fitar da iskar Carbon zuwa shekarar 2030, da kuma kawar da illar sa zuwa shekarar 2060, ba a kai ga biyan bukatun ba bisa karfin kasar Sin ta fannin sabbin makamashi. Hukumar makamashi ta duniya (IEA) ta yi gargadin cewa, har yanzu ana yawan amfani da makamashi irinsu kwal, da mai da iskar gas, don haka ma, kalubalen da ake fuskanta ba wai na “ana samar da makamashi mai tsabta fiye da kima ba” ne, sai ma dai matsalar karancinsu.

Amurka ta na son shawo kan masana’antun samar da kayayyaki masu nasaba da sabbin makamashi na kasar Sin ne don kare masana’antun ta, amma hakan na dakile kokarin da sassan kasa da kasa ke yi na sake fasalin makamashin da ake amfani da su, tare da lalata moriyar kasashe masu tasowa, ta fannin tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

A hakika, cikin jirgi guda ne daukacin ‘yan Adam suke, kuma ba za a kai ga tinkarar kalubalen sauyin yanayi da suke fuskanta ba, har sai sun hada gwiwa da juna. (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaPhilippinesSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Philippines Ba Ta Da Imani Ko Kadan

Next Post

Hukumar NCAA Ta Karyata Rahoton Sayen Mota Ta Fiye Da Naira Miliyan 250

Related

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

7 days ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

2 weeks ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

2 weeks ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

2 weeks ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

3 weeks ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

3 weeks ago
Next Post
NCAA

Hukumar NCAA Ta Karyata Rahoton Sayen Mota Ta Fiye Da Naira Miliyan 250

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.