ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Kwanan nan, an gudanar da taron kasa da kasa kan makamashi karo na 26 a birnin Rotterdam na kasar Netherlands. Taken taron shi ne “A sake tsara fasalin makamashi ga dan Adam da duniya”, a daidai lokacin da duniya ke fuskantar kalubale na sake fasalin makamashin da ake amfani da su, taron ya jawo wakilai kusan dubu 20 daga sassan makamashi na duniya. Amin Nasser, babban darektan kamfanin Saudi Aramco mai samar da man fetur na kasar Saudiyya, ya yaba da gudummawar da kasar Sin ta samar ta fannin cimma burin samun daidaito tsakanin yawan hayaki mai dumama yanayi da za a fitar, da yawan abubuwan da za su shawo kan hayakin a fadin duniya. A cewarsa, ta hanyar rage kudin sarrafa farantan samar da wutar lantarki ta hasken rana, kasar Sin ta tallafa wa kasashen duniya, ciki har da kasashen yamma, wajen bunkasa sabbin makamashi, kuma abin haka yake ta fannin motoci masu aiki da lantarki. 

A lokacin da kasar Amurka ke ta zargin kasar Sin da cewa wai “ta wuce misali wajen samar da sabbin makamashi”, furucin na malam Amin Nasser ya jawo hankalin kasa da kasa, ba kawai sabo da matsayinsa da na kamfaninsa ta fannin makamashin duniya ba, har da ma adalci da ya yi kan rawar da kasar Sin ke takawa wajen samar da makamashi mai tsabta, da ma rage fitar da iskar Carbon.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Faransa Da Serbiya Gami Da Hungary
  • CMG Ya Gudanar Da Bikin Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Yayata Tasharsa Ta 8K UHD

A halin da ake ciki na kara samun zafin yanayi, da ma bala’u daga indallahi, yana ta kara zama dole a sake fasalin makamashi da ake amfani da su. Duk da haka, aikin ba shi da sauki. Don tabbatar da daidaiton kasa da kasa na tinkarar sauyin yanayin duniya, a cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta dogara ga kirkire-kirkiren fasahohi, da manyan kasuwanninta, da cikakken tsarin masana’antunta, kuma ta yi ta samun ci gaba ta fannin sabbin makamashi. Ban da biyan bukatun cikin gida, kayayyaki masu nasaba da sabbin makamashi da kasar Sin ta samar sun kuma samar da dama ga kasashen duniya, musamman ma kasashen Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa, wajen sauya makamashin da suke amfani da su da ma tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

ADVERTISEMENT

In mun duba kasashen Afirka, bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, kasar Sin ta aiwatar da shirye-shirye daruruwa na samar da wutar lantarki ta makamashi masu tsabta. A kasar Kenya, tashar samar da wutar lantarki da makamashin rana ta Garissa, wadda wani kamfanin kasar Sin ne ya gina, ta kasance mafi girma a gabashin Afirka, kuma bayan da aka fara aiki da ita a shekarar 2019, ta rika samar da wuta sama da KW miliyan 76 a kowace shekara, wadda ke iya biyan bukatun mutane sama da dubu 380, kana ta yi matukar saukaka matsalar karancin wutar lantarki da aka fuskanta a wurin. Sai kuma a Nijeriya, a watan Mayun bara, an fara aiki da bas-bas masu aiki da lantarki da kamfanin samar da bas-bas na kasar Sin ya samar, matakin da ke da matukar ma’ana ga tabbatar da dauwamammen ci gaban harkokin zirga-zirga, da ma sake fasalin makamashi a kasar da ma shiyyar yammacin Afirka baki daya. A ganin Adhere Cavince, masanin ilmin huldar kasa da kasa na kasar Kenya, kasar Sin ba kawai tana kokarin sauya makamashin da take amfani da su ba, har kullum tana kuma hada kai da kasashen Afirka, har ma ta zama babbar abokiyar hadin gwiwa ga kasashen Afirka, wajen bunkasa makamashin da ake samarwa ta hasken rana da kuma karfin iska.

Ya zuwa bara, shekaru 10 a jere ke nan kasar Sin tana kan matsayi na farko a duniya, wajen samar da wutar lantarki da sabbin makamashi. Ban da haka, kasar Sin ta kuma samar da kaso 50% na na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska, da kuma kaso 80% na na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana da ake bukata a duniya. A cikin shekaru 10 da suka wuce, matsakaicin kudin da ake bukata wajen samar da wutar lantarki ta karfin iska da ta hasken rana, ya ragu da kashi 60% da kuma 80% kowanensu, kuma hakan ba ya rasa nasaba da babbar gudummawar da kasar Sin ta bayar. A wata makala da kafar Bloomburg ta fitar, an ce, kayayyaki masu nasaba da sabbin makamashi da kasar Sin ta samar cikin farashi mai sauki, sun samar da damar sauya fasalin makamashin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Amma duk da haka, ko ta fannin cimma burin da aka saka a yarjejeniyar Paris, ko kuma ta cimma burin kasar Sin na kaiwa kololuwar fitar da iskar Carbon zuwa shekarar 2030, da kuma kawar da illar sa zuwa shekarar 2060, ba a kai ga biyan bukatun ba bisa karfin kasar Sin ta fannin sabbin makamashi. Hukumar makamashi ta duniya (IEA) ta yi gargadin cewa, har yanzu ana yawan amfani da makamashi irinsu kwal, da mai da iskar gas, don haka ma, kalubalen da ake fuskanta ba wai na “ana samar da makamashi mai tsabta fiye da kima ba” ne, sai ma dai matsalar karancinsu.

Amurka ta na son shawo kan masana’antun samar da kayayyaki masu nasaba da sabbin makamashi na kasar Sin ne don kare masana’antun ta, amma hakan na dakile kokarin da sassan kasa da kasa ke yi na sake fasalin makamashin da ake amfani da su, tare da lalata moriyar kasashe masu tasowa, ta fannin tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

A hakika, cikin jirgi guda ne daukacin ‘yan Adam suke, kuma ba za a kai ga tinkarar kalubalen sauyin yanayi da suke fuskanta ba, har sai sun hada gwiwa da juna. (Lubabatu Lei)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

MASU ALAKA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
NCAA

Hukumar NCAA Ta Karyata Rahoton Sayen Mota Ta Fiye Da Naira Miliyan 250

LABARAI MASU NASABA

Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.