• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kungiyar Tuntuba Ta Yankin Funtuwa(fcF) Ta Karrama Hadiza Bala Usman

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Kungiyar Tuntuba Ta Yankin Funtuwa(fcF) Ta Karrama Hadiza Bala Usman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi 11 ga watan Disamba 2022 ne Kungiyar Tuntuba ta yankin Funtua wadda aka fi sani da (Futua Consultative Forum) da ke Jihar Katsina ta gudanar da taronta na shekara-shekara inda ta karrama wasu fittatun ‘yan asalin jihar tare da kaddamar da Mujallar kungiyar mai suna ‘The Trumpet Magazine’, taron ya gudana ne a karkashin jagorancin Farfesa Abdulmunin Ibrahim.

A jawabinsa, shugaban kungiyar Dakta Zaharadeen Idris ya bayyana cewa, an kafa kungiyar ne a shekara 13 da suka gabata kuma cikin ayyukan da kungiyar ta fi ba karfi sun hada da bunkasa harkar ilimi, tattalin arzikin al’umma, kiwon lafiya, da horar da mata matasa sana’oin dogaro da kai, suna kuma cimma manufofin ne ta hanyar gudanar da gangamin fadakarwa inda suke gayyatar masana a bangarori daban-daban don su gabatar da mukaloli, suna kuma jagorantar nema wa matasa ayyukan yi a gwamatocin tarayya dana jihohi da ma kamfanoni masu zaman kansu.

  • EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

Dakta Zaharadeen Idris ya kuma kara da cewa, a wannan shekarar sun samar da Mujalla wadda ta bayar da karfi wajen bayar da rahottanin irin cigaban da aka samu Jihar Katsina musamman ma a yankin Funtuwa, akwai kuma mukaloli na yadda al’umma za su bunkasa harkar kiwon lafiyarsu a dukkan matakai.

Taken taron na wannan shekarar ya yi bayani ne a kan yadda gwamnati za ta bunkasa harkar samar da kiwon lafiya musamman ga mata a ‘yankunan karkara.

Shugaban kungiyar ya kuma bayyana cewa, sun gayyaci tsohuwar shugabar Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya, NPA, Hajiya Hadiza Bala Usman ne don ta jagoranci kaddamar da Mujallar su saboda yadda ta nuna kishin Jihar Katsina a lokacin da take a kan karagar shugabancin NPA.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Ya ce, ta samar da ayyukan cigaba da bunkasa rayuwar al’umma da dama a yankuna mazabun majalisar dattawa uku da ke a Jihar Katsina, ayyukan kuma sun hada da horar da matasa sana’oin dogaro da kai a garin Dangani na karamar hukumar Musawa, horar da mata hanyoyin tsaftace mjuhalli a garin Daura, samar da fittilun kan titi masu amfani da hasken rana a yankuna kananan hukumomin Musawa, Mutazu, Malumfashi, Kafur da Bakori haka an samar da irin wannan fitillun kan titi masu amfani da hasken rana na kananan hukumkomin Danja, Funtua, Kankara, Sabuwa da kuma Faskari.
Bayani ya kuma nuna cewa, Hajiya Hadiza Bala Usman ta dauki nauyin horas da mata da matasa sana’oin dogaro da kai a kan Anan Dandume da Funtua.

A bangaren ilimi kuwa, Hajiya Hadiza Bala Usman ta gina tare da yi wa wasu makarantu a sassan jihar kwaskwarima, wananna aiki ya shafi kusan dukkan kananan hukumomin Jihar gaba daya da kuma gyara asibitin masu fama da cutar yoyon fitsari da ke garin Babban Ruga ta Jihar Katsina.

Dakta Zaharadee Idris ya kuma tabbatar da cewa, Hadiza Bala Usman ta yi wadannan ayyuka kuma ga wannan yake son ganinsu yana iya zuwa garuruwan da aka zayyana don ya gane wa kansa, a kan nr kuma ya yi kra ga ‘yan asalin Jihar Katsina da suke rike da madafun iko a hukumomi da kamfanonin gwamnati a fadin tarayyar Nijeriya su jajirce wajen koyi da Hajiya Hadiza ta hayar samar da ayyukan cigaban ga al’umma Jihar.

A nata jawabin, Hajiya Hadiza Bala Usman, wanda ta samu wakilcin Tsohon Kwamishinan Fili da Safiyo na Jihar Katsina, Alhaji Abubakar Sada, ta nuna jin dadinta ne a kan ayyukan kungiyar, tana mai cewa, dole ta alakanta kanta da ayyukan kungiyar saboda yadda suka yi daidai da ra’ayoyinta na bunkasa rayuwar al’umma musamman mazauna yankunan karkara, ta ce, matasa na da matuka muhimmanci a kokarin bunkasa rayuwar al’umma musamman a wannan lokacin da ake fuskantar harkokin siyasa da zabubbukan 2023, a kan haka ta nemi Matasa su jajirce wajen ganin an gudanar da sahihin zabe su kuma gujewa shiga harkokin bangar siyasa da duk abin da zai kawo cikas ga zaman lafiya a jihar Katsina dama Nijeriya gaba daya.

Wadanda suka samu halartar taron sun hada da Shugaban Karamar Hukumar Funtua, Malam Lawal Sani Matazu, Farfesa Abdulmumi A Ibrahim da Babban Sakatare a ma’aikatar kudi da tsare-tsare na Jihar Katsina, Alhaji Hassan Musa da mataimakan shugabannin kananan hukumomin Faskari, Funtuwa, Kafur, Bakori, Malumfashi, Musawa, Matazu, da Kankara sauran sun hada da shugabannin sassa na kananam hukumomin Kafur, Funtuwa, Bakori, Danja, Matazu, haka kuma taron ya samu halartar Sarkin Maskan Katsina Hakimin Funtuwa Alhaji Sambo Idris Sambo wanda magajin Makera ya wakilta da sauran manyan malaman addini da ‘yan kasuwa da manyan malaman jami’oi daban-daban.

A yayin kaddamar da mujjalar kungiyar mai suna ‘The Trumpet, Hajiya Hadiza Bala Usman ta kaddamar da mujallar a kan kudi Naira Miliyan daya, ta kuma nemi manyan ma’aikatan gwamnati da manya ‘yankasuwa su tallafa wa kungiyar musamman ganin akidunta da ayyukanta sun shafi tallafa wa al’umma ne.

Bincike ya nuna cewa, Hajiya Hadiza Bala Usman ta gabatar ire-iren wadanan ayyukan bunkasa rayuwar al’umma a sassan jihohin tarayyar Nijeriya, wanda hakan ke kara tabbatar da tsananin kishin kasarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohuwa Mai Shekara 120 A Sakkwato

Next Post

Sin Na Adawa Da Siyasantarwa Ko Amfani Da Batun Yaki Da Ta’addanci A Matsayin Makami

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

3 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

4 weeks ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

4 weeks ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

4 weeks ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

4 weeks ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Sin Na Adawa Da Siyasantarwa Ko Amfani Da Batun Yaki Da Ta’addanci A Matsayin Makami

Sin Na Adawa Da Siyasantarwa Ko Amfani Da Batun Yaki Da Ta’addanci A Matsayin Makami

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don YaÆ™i Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don YaÆ™i Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
hadiza bala usman

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.