ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kungiyar Tuntuba Ta Yankin Funtuwa(fcF) Ta Karrama Hadiza Bala Usman

by Bello Hamza
4 years ago
hadiza bala usman

A ranar Lahadi 11 ga watan Disamba 2022 ne Kungiyar Tuntuba ta yankin Funtua wadda aka fi sani da (Futua Consultative Forum) da ke Jihar Katsina ta gudanar da taronta na shekara-shekara inda ta karrama wasu fittatun ‘yan asalin jihar tare da kaddamar da Mujallar kungiyar mai suna ‘The Trumpet Magazine’, taron ya gudana ne a karkashin jagorancin Farfesa Abdulmunin Ibrahim.

A jawabinsa, shugaban kungiyar Dakta Zaharadeen Idris ya bayyana cewa, an kafa kungiyar ne a shekara 13 da suka gabata kuma cikin ayyukan da kungiyar ta fi ba karfi sun hada da bunkasa harkar ilimi, tattalin arzikin al’umma, kiwon lafiya, da horar da mata matasa sana’oin dogaro da kai, suna kuma cimma manufofin ne ta hanyar gudanar da gangamin fadakarwa inda suke gayyatar masana a bangarori daban-daban don su gabatar da mukaloli, suna kuma jagorantar nema wa matasa ayyukan yi a gwamatocin tarayya dana jihohi da ma kamfanoni masu zaman kansu.

  • EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

Dakta Zaharadeen Idris ya kuma kara da cewa, a wannan shekarar sun samar da Mujalla wadda ta bayar da karfi wajen bayar da rahottanin irin cigaban da aka samu Jihar Katsina musamman ma a yankin Funtuwa, akwai kuma mukaloli na yadda al’umma za su bunkasa harkar kiwon lafiyarsu a dukkan matakai.

ADVERTISEMENT

Taken taron na wannan shekarar ya yi bayani ne a kan yadda gwamnati za ta bunkasa harkar samar da kiwon lafiya musamman ga mata a ‘yankunan karkara.

Shugaban kungiyar ya kuma bayyana cewa, sun gayyaci tsohuwar shugabar Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya, NPA, Hajiya Hadiza Bala Usman ne don ta jagoranci kaddamar da Mujallar su saboda yadda ta nuna kishin Jihar Katsina a lokacin da take a kan karagar shugabancin NPA.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Ya ce, ta samar da ayyukan cigaba da bunkasa rayuwar al’umma da dama a yankuna mazabun majalisar dattawa uku da ke a Jihar Katsina, ayyukan kuma sun hada da horar da matasa sana’oin dogaro da kai a garin Dangani na karamar hukumar Musawa, horar da mata hanyoyin tsaftace mjuhalli a garin Daura, samar da fittilun kan titi masu amfani da hasken rana a yankuna kananan hukumomin Musawa, Mutazu, Malumfashi, Kafur da Bakori haka an samar da irin wannan fitillun kan titi masu amfani da hasken rana na kananan hukumkomin Danja, Funtua, Kankara, Sabuwa da kuma Faskari.
Bayani ya kuma nuna cewa, Hajiya Hadiza Bala Usman ta dauki nauyin horas da mata da matasa sana’oin dogaro da kai a kan Anan Dandume da Funtua.

A bangaren ilimi kuwa, Hajiya Hadiza Bala Usman ta gina tare da yi wa wasu makarantu a sassan jihar kwaskwarima, wananna aiki ya shafi kusan dukkan kananan hukumomin Jihar gaba daya da kuma gyara asibitin masu fama da cutar yoyon fitsari da ke garin Babban Ruga ta Jihar Katsina.

Dakta Zaharadee Idris ya kuma tabbatar da cewa, Hadiza Bala Usman ta yi wadannan ayyuka kuma ga wannan yake son ganinsu yana iya zuwa garuruwan da aka zayyana don ya gane wa kansa, a kan nr kuma ya yi kra ga ‘yan asalin Jihar Katsina da suke rike da madafun iko a hukumomi da kamfanonin gwamnati a fadin tarayyar Nijeriya su jajirce wajen koyi da Hajiya Hadiza ta hayar samar da ayyukan cigaban ga al’umma Jihar.

A nata jawabin, Hajiya Hadiza Bala Usman, wanda ta samu wakilcin Tsohon Kwamishinan Fili da Safiyo na Jihar Katsina, Alhaji Abubakar Sada, ta nuna jin dadinta ne a kan ayyukan kungiyar, tana mai cewa, dole ta alakanta kanta da ayyukan kungiyar saboda yadda suka yi daidai da ra’ayoyinta na bunkasa rayuwar al’umma musamman mazauna yankunan karkara, ta ce, matasa na da matuka muhimmanci a kokarin bunkasa rayuwar al’umma musamman a wannan lokacin da ake fuskantar harkokin siyasa da zabubbukan 2023, a kan haka ta nemi Matasa su jajirce wajen ganin an gudanar da sahihin zabe su kuma gujewa shiga harkokin bangar siyasa da duk abin da zai kawo cikas ga zaman lafiya a jihar Katsina dama Nijeriya gaba daya.

Wadanda suka samu halartar taron sun hada da Shugaban Karamar Hukumar Funtua, Malam Lawal Sani Matazu, Farfesa Abdulmumi A Ibrahim da Babban Sakatare a ma’aikatar kudi da tsare-tsare na Jihar Katsina, Alhaji Hassan Musa da mataimakan shugabannin kananan hukumomin Faskari, Funtuwa, Kafur, Bakori, Malumfashi, Musawa, Matazu, da Kankara sauran sun hada da shugabannin sassa na kananam hukumomin Kafur, Funtuwa, Bakori, Danja, Matazu, haka kuma taron ya samu halartar Sarkin Maskan Katsina Hakimin Funtuwa Alhaji Sambo Idris Sambo wanda magajin Makera ya wakilta da sauran manyan malaman addini da ‘yan kasuwa da manyan malaman jami’oi daban-daban.

A yayin kaddamar da mujjalar kungiyar mai suna ‘The Trumpet, Hajiya Hadiza Bala Usman ta kaddamar da mujallar a kan kudi Naira Miliyan daya, ta kuma nemi manyan ma’aikatan gwamnati da manya ‘yankasuwa su tallafa wa kungiyar musamman ganin akidunta da ayyukanta sun shafi tallafa wa al’umma ne.

Bincike ya nuna cewa, Hajiya Hadiza Bala Usman ta gabatar ire-iren wadanan ayyukan bunkasa rayuwar al’umma a sassan jihohin tarayyar Nijeriya, wanda hakan ke kara tabbatar da tsananin kishin kasarta.

hadiza bala usman
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Sin Na Adawa Da Siyasantarwa Ko Amfani Da Batun Yaki Da Ta’addanci A Matsayin Makami

Sin Na Adawa Da Siyasantarwa Ko Amfani Da Batun Yaki Da Ta’addanci A Matsayin Makami

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.