• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
9 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da Nijeriya ke ci gaba da fusknatar kalubalen tattalin arziki da kuma hauhawar farashin kaya, wanda aka ruwaito cewa; shi ne mafi kamari a cikin shekaru 17 da suka wuce, hakan ya kuma shafi masu sana’ar kiwon kajin gidan gona, inda wasu masu sana’ar a Jihar Kano; tsadar ‘yan tsakin da abincinsu ta tilasata su dakatar da sana’ar.

 

Wani daga cikin masu sana’ar a jihar, Bala Idris ya sanar da cewa; tuni wasu daga cikinsu suka durkushe, sakamakon wannan matsala; inda wasu kuma da dama ke ci gaba da fafutukar lalubo mafita dangane da wannan kalubale da fannin ke fuskanta a jihar.

  • Rikicin PDP: A Daina Maganar Tsayawa Takarar Shugaban Kasa A 2027, A Maida Hankali Kan Jam’iyya –Saraki
  • Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma’aikatan Filato

Wasu masu sana’ar kuma su ma sun bayyana cewa, farashin abincin kaji da kuma na ‘yan tsakin; ya fi tashi a cikin watan Nuwamba zuwa watan Disamba, amma a cikin wannan shekarar; tashin farashin ya fi yin kamari matuka, sabanin shekarun baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Wasu masu ruwa da tsaki a fannin da ke a jihar, Yakubu Ibrahim; wanda ke da gonar kiwon kajin da ake kira ‘Albarka’ ya sanar da cewa, saboda kalubalen biyu a yanzu, baya iya gudanar da aikin kamar a baya, inda ya kara da cewa; a baya ba su taba fuskantar irin wannan kalubale ba.

 

Ibrahim ya ce, akwai abubuwa da dama da suka jawo hakan wadanda suka hada da tsadar kajin da abincinsu, inda hakan ya jawo wasu ke barin ko ficewa daga sana’ar.

 

Ya kara da cewa, ana kuma fuskantar kalubalen masu yin kyankyasar ‘yan tsaki a jihar, inda ya kara da cewa; daukacin ‘yan tsakin ana shigo da su ne daga kudancin kasar nan, domin akasari ba a cika samun kamfanonin da ke yin kyankyasar ‘yan tsakin a jihar ba.

 

Ibrahim ya kara da cewa, masu kiwon kajin da ake kira da ‘Broilers’ a turance a jihar, su ne suka fi fuskantar wannan kalubale; domin farashinsu ya tashi matuka, wanda kuma ba a taba ganin hakan a baya ba.

 

A cewarsa, akasarin hakan ya fi afkuwa a lokacin bukukuwan karshen shekara da kuma lokacin gudanar da bikin Kirismeti, domin masu kiwon suna ci gaba da kiwon nasu ne har tsawon wata uku ko hudu kafin ‘yan tsakin su girma.

 

“Masu kiwon kaji da ake kira ‘Broilers’ a turance a jihar, su ne suka fi fuskantar wannan kalubale; domin farashinsu ya tashi matuka wanda kuma ba a taba ganin hakan a baya ba”.

 

Bincike ya nuna cewa, a yanzu haka ana kara samun bukatar kajin, inda hakan kuma ya shafi rabar da kajin a yankunan Arewa.

 

A yanzu dai, ana sayar da ‘yan tsakin kyankyasar kwana daya a kan Naira 800, inda kuma ba a iya sayen ‘yan tsakin da aka kyankyashe a cikin sati biyu ganin cewa kowane daya ana sayarwa a kan Naira 1,000; kuma babu wanda zai yarda ya sayi kowane daya a kan Naira 2,000.

 

Shi ma wani mai ruwa da tsaki a fannin, Mansur Shehu Kiru; mai gonar kiwon kajin da ake kira da ‘Rahama Agro’ ya bayyana cewa, ya rage yawan kajin daga 2,000 zuwa 400, sakamakon tsadar safararsu daga garin Ibadan zuwa Kano.

 

Ya ci gaba da cewa, magungunan kajin ma sun yi tashin gwauron zabi, inda ya kara da cewa; wannan ma babban kalubale ne da masu sana’ar ke fusktanta a jihar.

 

Ya ce, a ‘yan tsakin na ‘broiler’ a shekarar da ta wuce, ana sayar da duk guda daya a kan Naira 500; amma yanzu farashin ya kai daga Naira 800 zuwa Naira 850.

 

Mansur Shehu, a baya ana sayar da buhun abincin ‘yan tsakin a kan Naira 3,500, amma yanzu farshin ya kai daga Naira 8,000 zuwa Naira 9,000.

 

Shi ma wani mai ruwa da tsaki a fannin, Zaharaddin Yakasai; wanda ke da gonar kiwon da ake kira da ‘Yaks’ a Jihar Kano ya sanar da cewa, abincin kajin ya yi matukar tsada a bana, musamman saboda matsin tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.

 

Zaharaddin Yakasai ya bayyana cewa, saboda wadannan kalubale wasu masu sana’r suka dakatar da ita, domin tafiyar da fannin a halin yanzu; akwai matukar wahala.

 

Ya sanar da cewa, idan ka lissafa za ka ga ba wata ribar kirki muke samu ba, inda ya ce; wasu na barin sana’ar wasu kuma sun rage yawan adadin wadanda suke kiwatawa.

 

A cewar Zaharaddin Yakasai, muna matukar bukatar gwamnati ta kawo mana dauki, musamman ganin yadda fannin ke taimakawa wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a jihar, musamman a tsakanin matasan jihar.

 

Zaharaddin Yakasai, ya kuma koka a kan yadda duk da wadannan kalubale da masu sana’ar ke ci gaba da fuskanta, amma masu karbar haraji tun daga kananan hukomomi har zuwa matakin jiha; ba sa daga musu kafa, inda ya sanar da cewa; masu karbar harajin na karbar daga Naira 100,000 zuwa Naira 300,000.

 

“Akwai matukar bukatar gwamnati ta kawo mana dauki, musamman ganin yadda fannin ke taimakawa wajen samar da ayyukan yi kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a jihar, musamman a tsakanin matasa”.

 

Shi ma, wani dilan ‘yan tsaki da sauran tsintsaye a jihar; Abdurrahman Suleiman Tarauni ya bayyana cewa, sana’ar a halin yanzu ba ta tafiya yadda ya kamata, inda ya kara da cewa; a yanzu ana sayar da abincin kajin daga Naira 8,000 zuwa Naira 9,000, inda hakan ya sa mutane ba sa iya saya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Kiwon Dabbobi Sun Jinjina Wa Cibiyar Binciken Dabbobi Ta Nijeriya

Next Post

Abin Da Ya Sa Masu Saye Da Sayar Da Amfanin Gona A Kaduna Suka Ragu

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

12 hours ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

13 hours ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Dawanau

Abin Da Ya Sa Masu Saye Da Sayar Da Amfanin Gona A Kaduna Suka Ragu

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.