• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matasa Ke Kara Shiga Harkar Tsaface-tsaface

by Leadership Hausa
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Matasa Ke Kara Shiga Harkar Tsaface-tsaface
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai marasa dadin ji, na ci gaba da karade shafukan yada labarai na zumunta kan yadda kusan jiddan walahairan, mahukunta ke ci gaba da kama wasu matasa marasa imani, dauke da wasu sassan jikin ‘yan Adam, wadanda ake hasashen, suna aikata haka ne, da nufin aikata ayyukan asiri, musamman domin su zama masu arziki, a dare daya.

A farkon 2025, an cafke wani mai shekara 32 bisa zargin kashe wata buduwarsa’yar shekara 24, da yin aikin mai yiwa kasa hidima wato NYSC a Nicon Insurance Abuja.

  • Hukuma Ta Rufe Gidajen Gala A Jihar Kano
  • Gwamnatin Kano Za Ta ÆŠau Nauyin ÆŠalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje

Ba jima ba kuma, ‘yansanda suka kama wasu a yankin Ogil, na karamar hukumar Okigwe a jihar Imo, da ake zargi, dauke da Kokon kan bil Adama.

Duk dai a 2025, jami’an tsaro na ‘yan sa kai, a jihar Ogun, suka cafke, wani dan shekara 54, mai suna Adelani Oriyomi a makabartar da ke a yankin Kere, Obada-Oko, a garin Abeokuta, na jihar, bisa zargin yunkurin zakolo Kokon kan mamaci, daga cikin Kabari.

Wadannan sune wasu daga cikin rahotannin irin rashin imanin da aka wallafa, a wannan shekarar kadai.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

A 2024, rundunar ‘yansanda ta Abuja, sun kama wani mai suna Nuhu Ezra, a yanikin Lugbe dauke da Kokon kan mutum da Kasuwansa, inda wanda ake zargin, ya yi ikirarin cewa, ya ci karo da Kokon kan mutum da Kasuwan ne, a yayin da yake yin farauta a cikin Dajin Kuje.

Kazalika, duk dai a 2024, rundunar ‘yansanda ta jihar Ondo, sun cafke wani mai suna Yusuf Adenoyin, a yankin Isua, na karamar hukumar Akoko ta kudu maso gabas dauke da Kokon kan bil Adama guda takwas.

A Jihar Oyo ma, rundunar ‘yansanda ta jihar ta kama wasu mutane biyu a yankin Amuloko da ke garin Ibadan, bisa zargin samun dauke da danyen Kokon kan wata mata , da ba a san kowacce ba.

A 2023, mutane biyar kowannen su Kotu ta yankewa hukuncin zama gidan kaso na shekaru sha biyu, bayan sun amsa laifin na tuno Kokon kan bil Adama a Kabari, bisa umarnin Bokansu da ya yi masu alkawarin mayar da su masu kudi.

Duk dai a 2023, kakakin rundunar ‘yansanda ta jihar Neja DSP Wasiu Abiodun, a cikin sanarwar da ya fitar a jihar ya bayyana cewa, rundunar ta cafke wasu mutane biyar bisa zargin samun su dauke da Kokon kan mutum.

Ya ce, bayan rundunar ta bincike su, suka amsa cewa, wani Bokansu su ne, ya umarce su samo Kokon kan mutum don ya hada masu asiri su zama masu kudi, inda ya kara da cewa, sai dai Bokan ya arce.

Wannan rashin imanin na irin wadannan matasan har ya kai ga ya zama tamkar sana’a a tsakaninsu, musamman suna ganin ta hanyar ciro wasu sassan jikin ‘yan Adama ne, hanya mafi sauki a gare su, domin su zama masu arziki.

Lamarin na bakin ciki, sai kara zama ruwan dare yake yi a tsakanin wasu matasan kasar.

Wannan lamarin ya tuna mana da Clifford Orji fitaccen rikakken dan kungiyar asiri da ‘yansandan jihar Legas suka kama a ranar 3 na watan Fabirairun 1999. Orji, ya yi kaurin suna wajen sace mutane, musamman mata domin aikata ayyukan asiri.

Batun cire sassan jikin ‘yan Adama domin aikata asiri a kasar nan, kusan za a iya cewa, maimakon irin wannan dabbacin ya ragu, kusan za a iya cewa, karuwa ma yake kara yi a kasar, wanda za a iya danganta karuwar lamarin kan rashin daukar hukunci na doka kan lokaci, inda har a wani lokacin a kanga irin wanda ake zargin da aikata wannan ta’asar, suna ci gaba da yawon su a cikin alumma ba tare da an hukunta su, bisa doka ba

Dole ne a sauya irin wannan halin na rashin hukunta wadanda ake zargin domin mutane na bukatar sanin, shin yaushe ne, aka kama irin wadannan mutane da ake zargin su aikta wannan rashin imanin, shin an gurfanar da su a gaban Kuliya, domin yin haka ne kawai zai tabbatar da girmama dokar kasa da fito da mutatun kasar nan da kuma daidaita al’amura.

Akwai matukar bukatar wayar da kan matasa domin a sauya tunaninsu zuwa aikata dabi’u masu kyau, musamma domin a cire masu tunanin son yi arziki a cikin gaggawa, musamman ta hanyar kirkiro da shirye-shiryen wayar masu da kai, da kuma sanya shirye-shiryen a cikin manhajar karatun zamani don a rinka ilimanatar da su, kan illar son zama masu arziki, a cikin dare daya.

Kazalika, akwai gagarumar gudunmawar da Malaman addinai da Sarakunan Garjajiya za su bayar a matsayinsu na shugabannin alumma wajen ilimantarwa da fadakarwa, musamman a tsakanin matasa kan illar son yin arziki a dare daya.

Wannan zai iya faruwa ne kawai, idan shugabanin suma sun kasance masu hali na gari.

Bugu da kari dole ne gwamnati ta samar da ababen more rayuwa da samar da kyakyawan yanayi ga ‘yan kasar, musamman duba da yadda rashin aikin yi, musamman a tsakanin matasan kasar ya zama ruwan dare a kasar.

Dole ne kuma gwamnatin ta rage ci gaba da fifita bangaren masu arziki kuma dole ta sani cewa, tsare-tsaren da ta fito da su da ke shafar rayuwar manyan mutane, haka suna shafar rayuwar matsakaitan alumomin kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MatasaTsafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin

Next Post

Abubuwan Da Suka Ta Da Kura A Litttafin Janar Babangida

Related

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da É—umi-É—uminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

4 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

8 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

9 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

16 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

22 hours ago
Tattalin ArziÆ™in Nijeriya Ya BunÆ™asa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin ArziÆ™in Nijeriya Ya BunÆ™asa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

1 day ago
Next Post
Abubuwan Da Suka Ta Da Kura A Litttafin Janar Babangida

Abubuwan Da Suka Ta Da Kura A Litttafin Janar Babangida

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.