• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina – Ibrahim Masari 

by El-Zaharadeen Umar
7 months ago
in Labarai
0
Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina – Ibrahim Masari 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Baban mai taimaka wa shugaban ƙasa a kan harkokin siyasa, Hon. Ibrahim Kabir Masari, ya bayyana dalilan da ya sa suka shiga suka fita shi da gwamna Dikko Raɗɗa aka soke aikin sake gina hanyar kankara zuwa Katsina daga hannun ɗan kwangilar.

Masari, ya yi wannan kalamai ne a Katsina a lokacin bikin raba shinkafar da gwamnatin tarayya ta bai wa Jihar Katsina domin raba wa al’umma su rage raɗaɗin rayuwa da ake fama da shi.

  • Ya Kamata Wike Ya Kyale Ribas Ta Zauna Lafiya – Fubara
  • An Kashe Dorinar Ruwa A Jihar Kebbi Bayan Ta Kashe Mai-Gadin Lambun Basarake

Wannan aikin hanyar mai tsawon kilo mita 170 da ta taso daga marabar kankara zuwa Katsina ta haɗa ƙananan hukumomi bakwai da yawansu manoma ne sannan suna fuskantar matsalar tsaro daga ‘yan bindiga

Kamar yadda alkaluma suka nuna aikin wannan hanya zai ratsa kananan hukumomi guda 7 da suka haɗa da Malumfashi da Kankara da Ɗanmusa da Safana da Dutsinma da Kurfi da kuma Ɓatagarawa a Jihar Katsina.

Lokaci da aka ba da aikin wannan hanya al’umma da dama sun nuna farin cikinsu da samun wannan aiki wanda suka bayyana cewa zai taimaka wa al’umma musamman manoma sannan zai taimaka wa jami’an tsaro wajen kai ɗauki a yayin da aka kai hari wuce gona da iri.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

Sai dai kwatsam aka ji labarin ministan ayyuka na Nijeriya ya soke wannan kwangila daga hannun kamfanin da aka bai wa ita daga farko duk da cewa an fara aikin.

Shi ma a nasa jawabin babban mai taimaka wa shugaban kasa a harkokin siyasa Hon Ibrahim Masari ya bayyana wasu hanyoyi da gwamnatin tarayya ta bada aikinsu, sai dai ya ce hanyar kankara zuwa Katsina ba a ɗora ƙwarya a gurbinta ba shi ya sa suka je wajen shugaban ƙasa domin ya soke ta.

Ana dai zargin cewa wani jigo ne a jam’iyar PDP a Katsina kuma ɗaya daga cikin yaran Ministan Abuja, Nyesom Wike aka bai wa kwangilar aikin hanyar tun farko, lamarin da bai yi masu daɗi ba, inda suka shiga suka fita aka dakatar da aikin, wanda yanzu ba a san matsayin da aikin hanyar yake ciki ba.

Yanzu dai abin jira a gani shi ne, ko shugaban ƙasa zai sake ba da aikin hanyar a wani kamfanin da gwamna Dikko Raɗɗa da Hon. Ibrahim Kabir Masari suke so ko kuwa shike nan ruwa ta sha?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiKatsinaKwangila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Wike Ya Kyale Ribas Ta Zauna Lafiya – Fubara

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

Related

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

1 hour ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

3 hours ago
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi
Labarai

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

4 hours ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

5 hours ago
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
Manyan Labarai

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

6 hours ago
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

18 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.