• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
sallah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sallah karama, ibada ce da Musulmi ke gabatar da ita bayan kammala Azumin Ramadana, Sallar da wasu kuma ke kiranta Sallar ado, ta yadda za a ga kowane magidanci ya yi iya bakin kokarinsa na ganin ya faranta wa iyalansa ta hanyar yi musu dinkin kayan sawa domin fita kunya, da kuma shirya kayan abinci na musamman wanda sai a irin wannan rana ake sayensu.

To sai dai a wannan shekarar duk wanda ka kusanta sai ka ji yana kukan halin kuncin rayuwa da yadda al’amura suka lalace ta fuskar tattalin arziki, abin da mutum ya saya a shekarar da ta gabata a yanzu a kasuwa ya ninka sau uku. Wasu duk da halin da ake ciki sun yi iya kokarinsu wajen ganin sun yi wa ‘ya’yansu abin da ba a rasa ba. kafi a zo wannan yanayin magidanci yakan hakura da yi wa kansa dinki ya yi wa ‘ya’ya da matarsa, amma a wannan yanayin iyayen ne gaba daya suke hakuri da dinka kaya a yi wa yara, maganar abinci kuwa sai abin da aka gani.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Tsaraba Ga Amaren Bayan Sallah Da Masu Niyyar Aure

Wannan ta sa LEADERSHIP HAUSA ta zagaya wasa sassa na Abuja domin jin ta bakin wasu daga cikin mutane inda suka fadi albarkacin bakinsu. Muhammad Banufe wani mazaunin garin Mararraba ne da ke Jihar Nasarawa, cewa ya yi shi a yanzu, ba ya tunanin yin abinci da nama domin a yanzu kazar gidan gona kwaya daya ana sayar da ita Naira dubu 13, don haka shi ya hakura da yin abincin Sallah da nama.
“Yanzu fa kudin Zobo shi ne ya zama kudin shinkafa, kawai ka je ka sa a yi maka tuwon shinkafa miyar wake ka ci kawai ka hakura lamarin ya fi karfin tunaninka,” in ji shi.

Haka shima malam Haruna wani mazaunin cikin Abuja cewa ya yi a halinzu da rayuwa ta yi tsada ana kokarin abin da za a ci ne kawai dinki kuwa sai dai a yi wa yara su sa shi ma don kada yaro ya yi ta yi maka kuka ne. “Yanzu an samu canji sosai abubuwa sun ninka sau uku, abin da Naira dubu 10 za ta yi maka a shekarar da ta gabata yanzu sai ka sa Naira dubu 30, yadin da talaka zai saya wa dansa Naira 700, yanzu fa Naira 3000, to haka na 10,000 shi ne ya koma 30,000,” in ji shi.

Haka nan wani matukin KEKE NAPEP da bai bayyana sunansa ba cewa ya yi, a shekarar da ta gabata Naira dubu 13 ne suka isa ya sayi yadin da ya dinka wa ‘ya’yansa kayan Sallah su uku, amma a wannan shekarar dan karanin dansa ne ya cinye Naira dubu sha ukun shi kadai a dinkin ban da maganar takalmi da hula.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Wani matashi kuwa da ko aure bai yi ba cewa ya yi, dyk ba shi da aure amma yana tausayin masu iyali, saboda duk da ba shi da ‘ya’ya ya san masu ‘ya’ya suna fuskantar kalubale. “To ai gani na yi daga ni sai cikina amma ka duba yadda nake fama, koda yake na yi wa Allah godiya ina da iyaye kuma ina taimaka musu, amma da na duba kudin da na kashe wajen yi wa kannena kayan Sallah da abin da na saya na abin da za a ci sai na ga lallai magidanta suna cikin halin ni ‘ya su. tunanin da na yi shi ne da kuma a ce ba ni da shi fa yaya zan yi, sannan kuma magidantan da basu da shi kuma yaya za su yi?” in ji shi.

Sau da dama Sallah karama ko babba ta kan samu al’umma musamman talakawa a irin wannan yanayi amma ba a taba shiga halin matsin rayuwa kamar wannan lokacin ba, rayuwar talaka dai a wannan lokaci sai dai addu’ar Allah ya kawo dauki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Hada-hadar Kasuwanci Da Ciniki Ta Sin Da Amurka Sun Gudanar Da Taron Mataimakan Ministoci Na Farko

Next Post

An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
sallah
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.