• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

byRabi'u Ali Indabawa
2 years ago
sallah

Sallah karama, ibada ce da Musulmi ke gabatar da ita bayan kammala Azumin Ramadana, Sallar da wasu kuma ke kiranta Sallar ado, ta yadda za a ga kowane magidanci ya yi iya bakin kokarinsa na ganin ya faranta wa iyalansa ta hanyar yi musu dinkin kayan sawa domin fita kunya, da kuma shirya kayan abinci na musamman wanda sai a irin wannan rana ake sayensu.

To sai dai a wannan shekarar duk wanda ka kusanta sai ka ji yana kukan halin kuncin rayuwa da yadda al’amura suka lalace ta fuskar tattalin arziki, abin da mutum ya saya a shekarar da ta gabata a yanzu a kasuwa ya ninka sau uku. Wasu duk da halin da ake ciki sun yi iya kokarinsu wajen ganin sun yi wa ‘ya’yansu abin da ba a rasa ba. kafi a zo wannan yanayin magidanci yakan hakura da yi wa kansa dinki ya yi wa ‘ya’ya da matarsa, amma a wannan yanayin iyayen ne gaba daya suke hakuri da dinka kaya a yi wa yara, maganar abinci kuwa sai abin da aka gani.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Tsaraba Ga Amaren Bayan Sallah Da Masu Niyyar Aure

Wannan ta sa LEADERSHIP HAUSA ta zagaya wasa sassa na Abuja domin jin ta bakin wasu daga cikin mutane inda suka fadi albarkacin bakinsu. Muhammad Banufe wani mazaunin garin Mararraba ne da ke Jihar Nasarawa, cewa ya yi shi a yanzu, ba ya tunanin yin abinci da nama domin a yanzu kazar gidan gona kwaya daya ana sayar da ita Naira dubu 13, don haka shi ya hakura da yin abincin Sallah da nama.
“Yanzu fa kudin Zobo shi ne ya zama kudin shinkafa, kawai ka je ka sa a yi maka tuwon shinkafa miyar wake ka ci kawai ka hakura lamarin ya fi karfin tunaninka,” in ji shi.

Haka shima malam Haruna wani mazaunin cikin Abuja cewa ya yi a halinzu da rayuwa ta yi tsada ana kokarin abin da za a ci ne kawai dinki kuwa sai dai a yi wa yara su sa shi ma don kada yaro ya yi ta yi maka kuka ne. “Yanzu an samu canji sosai abubuwa sun ninka sau uku, abin da Naira dubu 10 za ta yi maka a shekarar da ta gabata yanzu sai ka sa Naira dubu 30, yadin da talaka zai saya wa dansa Naira 700, yanzu fa Naira 3000, to haka na 10,000 shi ne ya koma 30,000,” in ji shi.

Haka nan wani matukin KEKE NAPEP da bai bayyana sunansa ba cewa ya yi, a shekarar da ta gabata Naira dubu 13 ne suka isa ya sayi yadin da ya dinka wa ‘ya’yansa kayan Sallah su uku, amma a wannan shekarar dan karanin dansa ne ya cinye Naira dubu sha ukun shi kadai a dinkin ban da maganar takalmi da hula.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Wani matashi kuwa da ko aure bai yi ba cewa ya yi, dyk ba shi da aure amma yana tausayin masu iyali, saboda duk da ba shi da ‘ya’ya ya san masu ‘ya’ya suna fuskantar kalubale. “To ai gani na yi daga ni sai cikina amma ka duba yadda nake fama, koda yake na yi wa Allah godiya ina da iyaye kuma ina taimaka musu, amma da na duba kudin da na kashe wajen yi wa kannena kayan Sallah da abin da na saya na abin da za a ci sai na ga lallai magidanta suna cikin halin ni ‘ya su. tunanin da na yi shi ne da kuma a ce ba ni da shi fa yaya zan yi, sannan kuma magidantan da basu da shi kuma yaya za su yi?” in ji shi.

Sau da dama Sallah karama ko babba ta kan samu al’umma musamman talakawa a irin wannan yanayi amma ba a taba shiga halin matsin rayuwa kamar wannan lokacin ba, rayuwar talaka dai a wannan lokaci sai dai addu’ar Allah ya kawo dauki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version