ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
sallah

Sallah karama, ibada ce da Musulmi ke gabatar da ita bayan kammala Azumin Ramadana, Sallar da wasu kuma ke kiranta Sallar ado, ta yadda za a ga kowane magidanci ya yi iya bakin kokarinsa na ganin ya faranta wa iyalansa ta hanyar yi musu dinkin kayan sawa domin fita kunya, da kuma shirya kayan abinci na musamman wanda sai a irin wannan rana ake sayensu.

To sai dai a wannan shekarar duk wanda ka kusanta sai ka ji yana kukan halin kuncin rayuwa da yadda al’amura suka lalace ta fuskar tattalin arziki, abin da mutum ya saya a shekarar da ta gabata a yanzu a kasuwa ya ninka sau uku. Wasu duk da halin da ake ciki sun yi iya kokarinsu wajen ganin sun yi wa ‘ya’yansu abin da ba a rasa ba. kafi a zo wannan yanayin magidanci yakan hakura da yi wa kansa dinki ya yi wa ‘ya’ya da matarsa, amma a wannan yanayin iyayen ne gaba daya suke hakuri da dinka kaya a yi wa yara, maganar abinci kuwa sai abin da aka gani.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Tsaraba Ga Amaren Bayan Sallah Da Masu Niyyar Aure

Wannan ta sa LEADERSHIP HAUSA ta zagaya wasa sassa na Abuja domin jin ta bakin wasu daga cikin mutane inda suka fadi albarkacin bakinsu. Muhammad Banufe wani mazaunin garin Mararraba ne da ke Jihar Nasarawa, cewa ya yi shi a yanzu, ba ya tunanin yin abinci da nama domin a yanzu kazar gidan gona kwaya daya ana sayar da ita Naira dubu 13, don haka shi ya hakura da yin abincin Sallah da nama.
“Yanzu fa kudin Zobo shi ne ya zama kudin shinkafa, kawai ka je ka sa a yi maka tuwon shinkafa miyar wake ka ci kawai ka hakura lamarin ya fi karfin tunaninka,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Haka shima malam Haruna wani mazaunin cikin Abuja cewa ya yi a halinzu da rayuwa ta yi tsada ana kokarin abin da za a ci ne kawai dinki kuwa sai dai a yi wa yara su sa shi ma don kada yaro ya yi ta yi maka kuka ne. “Yanzu an samu canji sosai abubuwa sun ninka sau uku, abin da Naira dubu 10 za ta yi maka a shekarar da ta gabata yanzu sai ka sa Naira dubu 30, yadin da talaka zai saya wa dansa Naira 700, yanzu fa Naira 3000, to haka na 10,000 shi ne ya koma 30,000,” in ji shi.

Haka nan wani matukin KEKE NAPEP da bai bayyana sunansa ba cewa ya yi, a shekarar da ta gabata Naira dubu 13 ne suka isa ya sayi yadin da ya dinka wa ‘ya’yansa kayan Sallah su uku, amma a wannan shekarar dan karanin dansa ne ya cinye Naira dubu sha ukun shi kadai a dinkin ban da maganar takalmi da hula.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Wani matashi kuwa da ko aure bai yi ba cewa ya yi, dyk ba shi da aure amma yana tausayin masu iyali, saboda duk da ba shi da ‘ya’ya ya san masu ‘ya’ya suna fuskantar kalubale. “To ai gani na yi daga ni sai cikina amma ka duba yadda nake fama, koda yake na yi wa Allah godiya ina da iyaye kuma ina taimaka musu, amma da na duba kudin da na kashe wajen yi wa kannena kayan Sallah da abin da na saya na abin da za a ci sai na ga lallai magidanta suna cikin halin ni ‘ya su. tunanin da na yi shi ne da kuma a ce ba ni da shi fa yaya zan yi, sannan kuma magidantan da basu da shi kuma yaya za su yi?” in ji shi.

Sau da dama Sallah karama ko babba ta kan samu al’umma musamman talakawa a irin wannan yanayi amma ba a taba shiga halin matsin rayuwa kamar wannan lokacin ba, rayuwar talaka dai a wannan lokaci sai dai addu’ar Allah ya kawo dauki.

sallah
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.