ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
sallah

Sallah karama, ibada ce da Musulmi ke gabatar da ita bayan kammala Azumin Ramadana, Sallar da wasu kuma ke kiranta Sallar ado, ta yadda za a ga kowane magidanci ya yi iya bakin kokarinsa na ganin ya faranta wa iyalansa ta hanyar yi musu dinkin kayan sawa domin fita kunya, da kuma shirya kayan abinci na musamman wanda sai a irin wannan rana ake sayensu.

To sai dai a wannan shekarar duk wanda ka kusanta sai ka ji yana kukan halin kuncin rayuwa da yadda al’amura suka lalace ta fuskar tattalin arziki, abin da mutum ya saya a shekarar da ta gabata a yanzu a kasuwa ya ninka sau uku. Wasu duk da halin da ake ciki sun yi iya kokarinsu wajen ganin sun yi wa ‘ya’yansu abin da ba a rasa ba. kafi a zo wannan yanayin magidanci yakan hakura da yi wa kansa dinki ya yi wa ‘ya’ya da matarsa, amma a wannan yanayin iyayen ne gaba daya suke hakuri da dinka kaya a yi wa yara, maganar abinci kuwa sai abin da aka gani.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Tsaraba Ga Amaren Bayan Sallah Da Masu Niyyar Aure

Wannan ta sa LEADERSHIP HAUSA ta zagaya wasa sassa na Abuja domin jin ta bakin wasu daga cikin mutane inda suka fadi albarkacin bakinsu. Muhammad Banufe wani mazaunin garin Mararraba ne da ke Jihar Nasarawa, cewa ya yi shi a yanzu, ba ya tunanin yin abinci da nama domin a yanzu kazar gidan gona kwaya daya ana sayar da ita Naira dubu 13, don haka shi ya hakura da yin abincin Sallah da nama.
“Yanzu fa kudin Zobo shi ne ya zama kudin shinkafa, kawai ka je ka sa a yi maka tuwon shinkafa miyar wake ka ci kawai ka hakura lamarin ya fi karfin tunaninka,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Haka shima malam Haruna wani mazaunin cikin Abuja cewa ya yi a halinzu da rayuwa ta yi tsada ana kokarin abin da za a ci ne kawai dinki kuwa sai dai a yi wa yara su sa shi ma don kada yaro ya yi ta yi maka kuka ne. “Yanzu an samu canji sosai abubuwa sun ninka sau uku, abin da Naira dubu 10 za ta yi maka a shekarar da ta gabata yanzu sai ka sa Naira dubu 30, yadin da talaka zai saya wa dansa Naira 700, yanzu fa Naira 3000, to haka na 10,000 shi ne ya koma 30,000,” in ji shi.

Haka nan wani matukin KEKE NAPEP da bai bayyana sunansa ba cewa ya yi, a shekarar da ta gabata Naira dubu 13 ne suka isa ya sayi yadin da ya dinka wa ‘ya’yansa kayan Sallah su uku, amma a wannan shekarar dan karanin dansa ne ya cinye Naira dubu sha ukun shi kadai a dinkin ban da maganar takalmi da hula.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Wani matashi kuwa da ko aure bai yi ba cewa ya yi, dyk ba shi da aure amma yana tausayin masu iyali, saboda duk da ba shi da ‘ya’ya ya san masu ‘ya’ya suna fuskantar kalubale. “To ai gani na yi daga ni sai cikina amma ka duba yadda nake fama, koda yake na yi wa Allah godiya ina da iyaye kuma ina taimaka musu, amma da na duba kudin da na kashe wajen yi wa kannena kayan Sallah da abin da na saya na abin da za a ci sai na ga lallai magidanta suna cikin halin ni ‘ya su. tunanin da na yi shi ne da kuma a ce ba ni da shi fa yaya zan yi, sannan kuma magidantan da basu da shi kuma yaya za su yi?” in ji shi.

Sau da dama Sallah karama ko babba ta kan samu al’umma musamman talakawa a irin wannan yanayi amma ba a taba shiga halin matsin rayuwa kamar wannan lokacin ba, rayuwar talaka dai a wannan lokaci sai dai addu’ar Allah ya kawo dauki.

sallah
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.