• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutuwar Abokai Biyu Ta Fallasa Lalacewar Asibitocin Jihar Neja

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Neja

Mutuwar tsohon kwaminisan yada labarai na Jihar Neja, Danladi Ndayebo da mashawarcin shugaban majalisar dattawa, Mohammed Isa ta fallasa lalacin kayayyakin lafiya a fadin jihar.

Abokan guda biyu sun samu mammunan hatsarin mota a kan hanyar Minna zuwa Suleja na Jihar Neja.

  • INEC Ta Roki ‘Yan Jarida Da Su Kauce Wa Labarai Da Dumi-Dumi Da Zafafan Kanun Labarai Don Jawo Hankali
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin Kungiyar APEC Karo Na 29

Rahotonni sun bayyana cewa sun mutu ne sakamakon sakacin jami’an lafiya da karacin kayayyakin aiki na bayar da agajin gaggawa da wadanda suka raunata.

Danladi ya mutu ne a ranar Litinin, yayin da Mohammed ya mutu a ranar Juma’a a cikin mako guda.

Kanin Danladi mai suna Usman Mohammed Ndayebo ya bayyana wa jaridar Daily Trust cewa dan’uwansa tare da Mohammed ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba lokacin da suke asibitin koyarwa na IBB da ke Minna har na tsawon awanni 13 da faruwar hatsarin. Ya ce allura kadai aka yi musu domin kashe zafin ciwon jikinsu bayan awanni hudu da suka isa asibitin.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Sakataren gwamnatin jihar, Ahmed Ibrahim Matane ya tabbatar da samun rahoton cewa mamatan guda biyu ba a ba su kulawar da ya kamata ba lokacin da aka kawo su asibitin.

“Na samu kiran waya da safe, inda aka shaida mun cewa Marigayi Ndayebo da wani majinyaci an garzaya da su asibitin koyarwa na IBB a cikin dare, amma abun takaici har zuwa da safe da aka kira ni babu wani likita da ya duba majinyatan.

“Babban abun takaicin shi ne, washagarin da safe lokacin da aka zo duba shi aka tarar ya mutu,” in ji Matane.

Ya ci gaba da cewa gwamnati ta damu da abun da ya faru na sakaci a asibitin gwamnati wanda bai kamata a samu irin hakan ba. Ya ce gwamnan jihar, Abubakar Sani Bello ya bayar da umurnin gudanar da sahihin bincike game da musabbabin mutuwar Ndayebo, a ga ko sakacin ne na jami’an asibitin koyarwa na IBB ko kuma rashin kwarewa ne.

A cewar bincike, mafi yawancin majinyata ciki har da mata masu juna biyu sun mutu a asibitin sakamakon karancin ma’aikata da za su gudanar da ayyuka, musamman ma ga wadanda suke bakatar kulawar gaggawa.

An dai bayyana cewa a wasu asibitocin, nas guda daya ke duba mara lafiya sama da 20 a cikin dare lokacin da karancin likitocin suka tashi daga aiki.

Idris Mohammed, wani majinyaci da aka kai shi babban asibitin Minni bayan samun hatsari ya ce ya fuskanci irin wannan lamari a can.

“Ina iya tuwa cewa an bukaci mu sayi safar hannu, amma muka ki wanda ya sa ma’aikatan jinyar suka dauki tsawon lokaci ba su duba ni ba. An dauki kwanaki biyu kafin likita ya duba ni. A duk lokacin da dan’uwana ya bukaci ganin likita, sai a ce masa lambarsa ba ya shiga,” in ji shi.

Binciken Daily Trust ya gano cewa likitoci guda hudu ne ke aiki a asibitin Jummai Babangida Maternal and Neonatal Hospital. Binciken ya bayyana cewa likitoci 500 ne a fadin jihar, amma likitoci guda 39 da ma’aikatan lafiya 800 sun gudu gaba jihar a cikin shekaru biyu.

Haka kuma binciken ya gano cewa a yanzu haka likitoci guda biyu ne kacal a babban asibitin Mokwa, yayin da a babban asibitin Bida akwai likitoci hudu, sannan a babban asibitin Kutigi akwai likita daya, a babban asibitin Agaie akwai likitoci uku, inda a babban asibitin Lapai akwai likitoci biyu, haka kuma a babban asibitin Kuta akwai likitoci biyu.

Haka kuma a babban asibitin Kafin-Koro da babban asibitin Tunga-Magajiya da babban asibitin Bangi da kuma babban asibitin Nasko dukkansu likita daya kowannansu yake da shi, yayin da a Auna da Gulu suke da likitoci biyu-biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Next Post
Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.