• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutuwar Abokai Biyu Ta Fallasa Lalacewar Asibitocin Jihar Neja

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Rahotonni, Manyan Labarai
0
Yadda Mutuwar Abokai Biyu Ta Fallasa Lalacewar Asibitocin Jihar Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutuwar tsohon kwaminisan yada labarai na Jihar Neja, Danladi Ndayebo da mashawarcin shugaban majalisar dattawa, Mohammed Isa ta fallasa lalacin kayayyakin lafiya a fadin jihar.

Abokan guda biyu sun samu mammunan hatsarin mota a kan hanyar Minna zuwa Suleja na Jihar Neja.

  • INEC Ta Roki ‘Yan Jarida Da Su Kauce Wa Labarai Da Dumi-Dumi Da Zafafan Kanun Labarai Don Jawo Hankali
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin Kungiyar APEC Karo Na 29

Rahotonni sun bayyana cewa sun mutu ne sakamakon sakacin jami’an lafiya da karacin kayayyakin aiki na bayar da agajin gaggawa da wadanda suka raunata.

Danladi ya mutu ne a ranar Litinin, yayin da Mohammed ya mutu a ranar Juma’a a cikin mako guda.

Kanin Danladi mai suna Usman Mohammed Ndayebo ya bayyana wa jaridar Daily Trust cewa dan’uwansa tare da Mohammed ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba lokacin da suke asibitin koyarwa na IBB da ke Minna har na tsawon awanni 13 da faruwar hatsarin. Ya ce allura kadai aka yi musu domin kashe zafin ciwon jikinsu bayan awanni hudu da suka isa asibitin.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Sakataren gwamnatin jihar, Ahmed Ibrahim Matane ya tabbatar da samun rahoton cewa mamatan guda biyu ba a ba su kulawar da ya kamata ba lokacin da aka kawo su asibitin.

“Na samu kiran waya da safe, inda aka shaida mun cewa Marigayi Ndayebo da wani majinyaci an garzaya da su asibitin koyarwa na IBB a cikin dare, amma abun takaici har zuwa da safe da aka kira ni babu wani likita da ya duba majinyatan.

“Babban abun takaicin shi ne, washagarin da safe lokacin da aka zo duba shi aka tarar ya mutu,” in ji Matane.

Ya ci gaba da cewa gwamnati ta damu da abun da ya faru na sakaci a asibitin gwamnati wanda bai kamata a samu irin hakan ba. Ya ce gwamnan jihar, Abubakar Sani Bello ya bayar da umurnin gudanar da sahihin bincike game da musabbabin mutuwar Ndayebo, a ga ko sakacin ne na jami’an asibitin koyarwa na IBB ko kuma rashin kwarewa ne.

A cewar bincike, mafi yawancin majinyata ciki har da mata masu juna biyu sun mutu a asibitin sakamakon karancin ma’aikata da za su gudanar da ayyuka, musamman ma ga wadanda suke bakatar kulawar gaggawa.

An dai bayyana cewa a wasu asibitocin, nas guda daya ke duba mara lafiya sama da 20 a cikin dare lokacin da karancin likitocin suka tashi daga aiki.

Idris Mohammed, wani majinyaci da aka kai shi babban asibitin Minni bayan samun hatsari ya ce ya fuskanci irin wannan lamari a can.

“Ina iya tuwa cewa an bukaci mu sayi safar hannu, amma muka ki wanda ya sa ma’aikatan jinyar suka dauki tsawon lokaci ba su duba ni ba. An dauki kwanaki biyu kafin likita ya duba ni. A duk lokacin da dan’uwana ya bukaci ganin likita, sai a ce masa lambarsa ba ya shiga,” in ji shi.

Binciken Daily Trust ya gano cewa likitoci guda hudu ne ke aiki a asibitin Jummai Babangida Maternal and Neonatal Hospital. Binciken ya bayyana cewa likitoci 500 ne a fadin jihar, amma likitoci guda 39 da ma’aikatan lafiya 800 sun gudu gaba jihar a cikin shekaru biyu.

Haka kuma binciken ya gano cewa a yanzu haka likitoci guda biyu ne kacal a babban asibitin Mokwa, yayin da a babban asibitin Bida akwai likitoci hudu, sannan a babban asibitin Kutigi akwai likita daya, a babban asibitin Agaie akwai likitoci uku, inda a babban asibitin Lapai akwai likitoci biyu, haka kuma a babban asibitin Kuta akwai likitoci biyu.

Haka kuma a babban asibitin Kafin-Koro da babban asibitin Tunga-Magajiya da babban asibitin Bangi da kuma babban asibitin Nasko dukkansu likita daya kowannansu yake da shi, yayin da a Auna da Gulu suke da likitoci biyu-biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbokaiAsibitHatsariMutuwaNeja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Sarrafa Rogo Da Kwakwar Manja A Binuwe Na Fuskantar Tasku

Next Post

Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

Related

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

13 hours ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

22 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

2 days ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

3 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

3 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

3 days ago
Next Post
Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.