ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
APC

A ranar Talata ce, jam’iyya mai mulki ta APC ta fara gudanar da yakin neman zabenta a garin Jos Babbar Birnin Jihar Filato, domin tallata jam’iyyar ta yadda ‘yan Nijeriya za su sake zabenta a 2023.

Kamar yadda yakin neman zaben 2023 ya kankama, hankulan jam’iyyun siyasa da masu neman takara ya kamo kan tallata manufofinsu a kakafen sadarwa ta yadda za su saye zuciyar masu jefa kuri’a har ma su zabe su.

  • Masu Cutar Sikari Na Fuskantar Karin Kudin Magani Da Kashi 200
  • Da Dumi-Duminsa: Buhari Ya Tsige Fadah A Matsayin Darakta Janar Na NYSC

Sashe na 94 (1) na dokar zaben 2022 ya bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daman dage takunkumin yakin neman zabe tun a ranar 28 ga watan Satumbar 2022.

ADVERTISEMENT

Bisa tsarin dokar zaben 2022, wannan shi ne karo na farko da kasar nan ta samu damar gudanar da yakin neman zabe har na tsawon watanni biyar, inda a baya ayyukan jam’iyyun siyasa na gudanar da yakin neman zabe ya yi karanci.

Kafin dai hukumar INEC ta dage takunkumin fara yakin neman zabe, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da sauran wasu gwamnoni da ke cikin jam’iyyar sun yi zawarcin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan domin samun goyon bayansa a babban zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Tinubu tare da mataimakin takararsa, Sanata Kashim Shettima da gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun da AbdulRahman AbdulRazak na Jihar Kwara da Bello Matawalle na Jihar Zamfara da gwamnan Jihar Jigawa, Abubakar Badaru da kuma gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong wanda shi ne darakta janar na yakin neman zaben jam’iyyar duk suna daga cikin wadanda suka gana da Jonathan.

Haka kuma tsohon gwamnan Jihar Legas ya ziyarci tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo a Abeokuta da tsofaffin shugabanin kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Babangida da kuma Janar Abdulsalam Abubakar.

Tun da farko dai, jaddawalin ayyukan yakin neman zaben APC an dakatar da su ne bayan da aka samu rudani kan jerin sunayen mambobi 422 na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa.

An dai yi tsammanin cewa jam’iyyar ta samu nasarar dinke barakar wanda aka sake fitar da jerin wadansu sunaye na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa da kowa ya amince da shi.

Bayan an samu nasarar lallashin ‘ya’yan jam’iyyar da suka fusata, Shugaban Kasa,

Muhammadu Buhari ya kaddamar da kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC tare da amincewa da a zabi Tinubu domin ya gaje shi.

Ya ce zaben Tinubu zai karfafa nasarar da gwamnatinsa ta samu a matsayinsa na dan takara mai nagarta da kyakkyawan shugabanci wanda zai iya dorawa daga wurin da suka tsaya.

Bayan kaddamar da kwamitin yakin neman zaben, an dai samu karancin gudanar da yakin neman zabe a cikin jam’iyya mai mulki wanda ba a yi tsammanin hakan ba. An dai bayyana cewa dalilin da ya sa aka samu tsaikon dai shi ne, mafi yawancin daraktocin yakin neman zaben sun dokara ne da kasafin kudi na gudanar da lamarin. Sannan an bayyana cewa lokacin da aka kammala kasafin kudin, za a saki kudaden ga daraktocin nan take domin gudanar da harkokin yakin neman zabe.

Jam’iyyar APC ta fara gudanar da yakin neman zabenta ne a garin Jos Babban Birnin Jihar Filato a ranar 15 ga watan Nuwamba gabanin zaben 2023. Jam’iyyar ta gana da kungiyoyin manoma a Jihar Neja a ranar 7 ga watan Nuwamba, sannan ta kara wani ganawar irin wannan da kungiyar masu hakar ma’adanai a ranar 9 ga watan Nuwamba a Keffi na Jihar Nasarawa.

Jam’iyya mai mulki ta sake gudanar da irin wannan tattaunawa a Kalaba na Jihar Kuros Ribas a ranar 12 ga watan Nuwamba na yadda za ta fara gudanar da yakin neman zabe a garin Jos ranar 15 ga watan Nuwamba. Wannan yana zuwa ne bayan tattaunawa a Jihar Imo ranar 17, inda daga bisani ta gudanar da ganganminta a Jihar Delta ranar 19 ga watan Nuwamba.

Da yake jawabi a ranar Alhamin da ta gabata lokacin kaddamar da kwamitin tuntuba na yankin arewa maso yamma karkashin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Darakta Hon. Aminu Jaji ya bayyana cewa jam’iyyar ta cancanci yakin neman zabe mai tsari da zai bambanta da na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPPA, Rabi’u Kwankwaso da ke yankin arewa maso yamma.

A cewarsa, wannan lokacin ne da za a saka wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar da kuma mutanen yankin kudu maso yamma bisa yadda suka goyi bayan Shugaban Kasa Buhari a zabukan 2015 da 2019.

Jaji ya ce bisa goyon bayan Shugaba Buhari na tsawan mulkinsa shekara bakwai da rabi, yankin arewa maso yamma zai goyi bayan samun nasarar Tinubu/Shettima a zabe mai zuwa.

Ya dai bukaci mambobin kwamitin yakin neman zabe su yi aiki tukuru wajen ganin samun nasarar jam’iyyar APC a kowani mataki a kasar nan.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.