• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ruwan Sama Ya Kara Dagula Hanyoyin Mota A Daminar Bana

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Yadda Ruwan Sama Ya Kara Dagula Hanyoyin Mota A Daminar Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu matafiya daga wannan jiha zuwa waccan suna cikin halin ni ‘yasu musamman ma sun kwan da sani irin yadda halin hanyoyin Nijeriya suke ciki, abinda ke kara jagule lamura shine lokacin damina. Daga Abuja zuwa Kaduna, Umuahia-Ikot Ekpene, Calabar-Itu, Ado Ekiti-Ikere-Akure, hakanan  Makurdi zuwa Enugu  abin ya zama kamar tarkon mutuwa  domin ganin yadda yanayin hanyoyin suke, shi yasa ma mazauna wuraren suka bukaci  a kammala hanyar  Lakwaja zuwa Benin.

 

Da yake yanzu ana cikin halin damina lokaci ne da za aiya gane lalle Nijeriya na fama da karancin hanyoyi masu kayau.

  • Yawan Cinikayyar Waje Ta Sin A Fannin Hajoji Da Bayar Da Hidimomi Ya Karu Da Kaso 4% A Agusta
  • Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

Abubuwan da ka iya faruwa sanadiyar rashin hanyoyi masu kyau suna da yawa, suna kuma taimakawa wajen matsalolin da ake fuskanta, da suka hada da tattalin arziki, zamantakewa, da kuma muhalli.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

A Katari kan hanyaer Kaduna zuwa Abuja za‘a iya ganin irin yadda matsalolin wani abu daga cikin sinadaran more rayuwa suke.

 

Duk da yake ma’aikatar ayyuka ta kasa bada dadewa bane ta kawo kamfanin Julius Berger, aka kira dan kwangilar da aka ba kwangilar tun farko ya dawo bakin aiki, duk da hakan hanyar zuwa yanzu ta zama alakakai.Matafiya lokutta da dama suna shan wahala idan suna kan hanyar, yayin da wani lokaci tafiyar ta kan karu da awa uku zuwa hudu wani lokaci ma kilomita biyu ne na waurin da ya lalace,bama kamar lokacin damina.

 

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayar da labaran irin rasher ashen rayukan da aka yi saboda yawan hadurran da suke aukuwa akan hanyar.

 

Mark Shima,wanda shi direba ne a tashar mota ta  mahadar Command dake Kaduna ya nuna bukatar d ake da ita ta daukar matakin gaggawa wajen gyare- gyaren hanyoyi,inda yace rashin kyan hanya ya sa an yi  asarar rayuka musamman ma, a wani wuri da yake a gaban Jere.

 

A Jihar Sakkwato hanya daga Sakkwato zuwa Kebbi duk da yake dai ba mai tagwayen hanyoyi bane,ba a samun matsala sosai.Sai dai kuma hanyar Sakkwato zuwa Gusau ita ma tana bada matsaloli.Wasu ayyukan gyare da hukumomin gwamnati suka yi ya kara inganta wuraren , amma akwai wuraren da suke bukatar daukar mataki. Akwai wuraren da ake fuskantar matsaloli da suka hada da Tureta,Dange-Shuni, and Talata Mafara.HanyarThe Dange-Shuni  ana maida ta tagwayen hanyoyi wadda aka faro daga Sakkwato amma sai dai aikin yana tafiyar Hawainiya.Wani dierba mai suna Sani Auwalu ya bayyana yadda yake fama da gyaran motar shi saboda rashin kyau na hanyar, saboda duk lokacin da aka ce ya dawo daga tafiya dole ne sai ya yi bincike saboda ko akwai noti ko kusa da ta bata.

 

A Jihar Kano lamarin bai canza ba domin kuwa hanyar Sabon Titi da take babbar hanya ce da ta hada manyan garuruwa kamar Gwarzo Madobi da Dorayi, ta kasance wata hanya c eke taimakawa ta wuraren da suke da rami, sai dai maganar neman a bada nagoro da matasa ke yi. Mustapha Niga, da yake direba  wanda yake zama kusa da wuraren, ya yi kira da gwamnati ta dauki matakin da ya dace saboda kada ta kara lalacewa fiye da yadda take yanzu.

 

Jihar Zamfara ma tana da matsalolin saboda yanayin daminar da ake ciki ga kuma hanyoyin gwamnatin tarayya da ake aikin gina su da gyara.Funtua  zuwa Gusau (kilomita  97ne), Gusau  zuwa Sakkwato ( kilomita 225 km), yayin da Gusau zuwa Magami da Dansadau (kilomita 105) hanyoyin basu da kyau.Ayyukan da ake cikin yi sun kara sa ana shan wahala lokacin tafiye – tafiye.

 

Hanyoyin Jihar Katsina kamar ta Gidan Mutun daya da zata kai mutum zuwa babban birnin Jihar tana bukatar gyara ita ma.Mallam Zuberu Sani,da yake mazaunin wurin yace da farko an yi niyyar tagwayen hanyoyi amma daga baya sai aka bar aikin bayan an fara, hakan na samar da matsalaoli ga matafiya.

 

Jihar Borno abin can ma akwai ban takaici kan lamarin hanyoyi wadanda sun lalace da maganar ambaliyar ruwa. Wannan shi yasa ake samun yawan harin’yan B  OKO Haram da garkuwa da jama’a.

 

A Jihar Neja kusan dukkan hanyoyin gwamnatin tarayya basu da dadin bi ayitafiya da mota lokacin damina.Hanyar Suleja zuwaMinna, Agaie-Baddegi-Bida,Kontagora-Rijau-Zuru, Kontagora-Bangi, Minna-Tegina, da Tegina-Bokani-Mokwa, da kuma Tegina zuwa Kalgara har da Birni Gwari  duk basu da kyau. Mista Samson Alfa ya ce saboda rashin kyau na hanyoyin yasa yasa kudin tafiya ya karu, ga kuma ambaliyar ruwa da zaizayar kasa.

 

A Jihar Kwara hanyoyin Ilorin-Omu-Aran-Egbe-Kabba da Share zuwa Patigi manyan matsaloli ne ga matafiya cewar Malam Ganiyu Adigbongbo,shugaban kungiyar direbobi ta kasa NURTW na reshen Gambari zuwa Ilorin, ya bayyana irin matsalolin da matafiya suke fuskanta.

 

Jihar Imo, hanyoyin Owerri zuwa Umuahia sune wadanda suka fi damuwar matafiya.Hanyar kuros riba ta Kudu maso gabas, da suka hada hanyoyin mazabun ‘yan majalisar dattawa uku na Jihar da kuma bangaren Neja Delta, suna da wurare biyu da basu da kyau.

 

Jihar Abia State hanyoyi kamar Umuahia-Ikot Ekpene da Aba-Ikot Ekpene sun dade da baci saboda yadda suke wahalar da matafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar Ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gudanar Da Bikin Bayar Da Lambobin Yabon Musayar Al’adu Na Sin Da Faransa A Shanghai

Next Post

Gwamna Ya Bukaci Sojoji Su Rika Amsa Kiran Gaggawa A Katsina

Related

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Labarai

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

39 minutes ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

3 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

6 hours ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

6 hours ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

7 hours ago
Next Post
katsina

Gwamna Ya Bukaci Sojoji Su Rika Amsa Kiran Gaggawa A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

May 22, 2025
Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

May 22, 2025
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.