ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
NBS

Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta bayyana cewa kashi 5.4 cikin 100 na ‘yan Ni-jeriya da suka kai miliyan 4,792,296 ba su da aikin yi a shekarar 2023.

Idan za a iya tuna dai, hukumar ta NBS a shekarar da ta gabata ta yi amfani da wa-ta sabuwar hanya ta binciken ma’aikata, inda ta ayyana wadanda ke cikin ma’aikata sun kai kashi 15 zuwa sama da haka, akwai kuma wadanda sun zarce haka idan aka fadada bincike.

  • Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
  • An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

A wata sanarwar manema labarai da aka wallafa a rubu’in farko na 2023 da rubu’in farko na farkon 2024 na sakamakon binciken ma’aikatan Nijeriya, NBS ta ce miliyan 116.6, wanda ke wakiltar kashi 53.8% na yawan al’ummar kasar ne ke cikin shekarun aiki.

ADVERTISEMENT

Sanarwar mai dauke da sa hannun daraktan sadarwa na hukumar NBS, Sunday. J Ichedi, ya ce mata ne ke da kashi 52 cikin dari na wannan al’umma, yayin da maza ke da kashi 48 cikin dari.

Yayin da aka yi nuni da cewa kashi 76.3 bisa dari kwatankwacin mutane miliyan 88.9 ne suka shiga cikin binciken, ya ce Jihar Bauchi ce ta fi kowacce yawan ja-ma’an da suka shiga wannan bincike da kashi 92.3, yayin da Jihar Ekiti ke da mafi karancin kashi 63.4 bisa dari.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya ci gaba da bayyana cewa jimlar yawan shekarun aiki a cikin 2023, mutane mili-yan 84.1 suke yin aiki, miliyan 20.6 daga ciki suna tsakanin shekaru 15 zuwa 24.

Sanarwar ta bayyana cewa, a rubu’in farko na shekarar 2024, yawan marasa ai-kin yi ya karu zuwa kashi 5.3 daga kashi 5.0 a cikin rubu’in farko na 2023, inda yankunan birane ke da kashi 6.0 cikin dari na rashin aikin yi, yayin da yankunan karkara ke da kashi 4.3 bisa dari.

“Yawancin ma’aikata a tsakanin masu shekarun aiki ya ragu zuwa kashi 77.3 a ci-kin rubu’in farko na 2024, daga kashi 79.5 cikin 100 na rubu’in farko na 2023. Yawan mutanen da ba su da aikin yi kai kashi 73.2 cikin 100 a rubu’in farko na 2024. An samu raguwar kashi 2.4 idan aka kwatanta da kashi 75.6 a cikin rubu’in farko na 2023.”

Rahoton ya kara da cewa adadin ma’aikatan da ke aikin albashi ya karu zuwa kashi 16.0 a cikin rubu’in farko na 2024, an samu karuwar kashi 3.3 idan aka kwatanta da kashi 12.7 da aka samu a rubu’in farko na 2023.

NBS
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
NBS
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ya Kamata Gwamnati Ta Kula Da Marayun Da Aka Bari Sanadin Mummunan Hatsarin Motar Lere – Sharif Danlami

Ya Kamata Gwamnati Ta Kula Da Marayun Da Aka Bari Sanadin Mummunan Hatsarin Motar Lere – Sharif Danlami

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.