• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Hadin Gwiwar Zamanantar Da Ayyukan Noma

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Hadin Gwiwar Zamanantar Da Ayyukan Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An sake samun girbi mai albarka a kasar Sin! Inda alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar a kwanan nan ta nuna cewa, a karon farko, kasar Sin ta kai ga cimma nasarar samun yawan hatsi da ya haura tan miliyan 700. Kafin hakan, cikin shekaru 9 a jere, kasar Sin na samun hatsin da ya haura tan miliyan 650 a duk shekara.

 

Bayan da muka watsa wannan labari ta shafinmu na Facebook, masu bibbiyarmu da dama sun taya kasar Sin murnar cimma wannan nasara. Hakika, har kullum masu bibbiyarmu na mai da hankali sosai a kan harkokin da suka shafi ci gaban noma a kasar Sin, musamman ma yadda kasar Sin ke zamanantar da ayyukan noma, wadanda kuma suke fatan ganin Sin da kasashen Afirka sun karfafa hadin gwiwarsu a wannan fanni.

  • Xi Ya Halarci Bikin Dawowar Yankin Musamman Na Macao Kasar Sin Da Rantsar Da Sabuwar Gwamnati
  • Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru

Hasali ma dai, ci gaban ayyukan noma sun tabbata ne sakamakon yadda kasar Sin ke ba da muhimmanci matuka a kan ayyukan da suka shafi noma da yankunan karkara da ma manoma. Kasar Sin kasa ce da yawan al’ummarta ya kai biliyan 1.4, haka kuma kasa ce da yawan manomanta ya kai kimanin miliyan 700. Don haka, batutuwa masu nasaba da noma da yankunan karkara da kuma manoma na shafar samar da abinci ga ‘yan kasar biliyan 1.4 da ma ci gaban kasar, kuma tunanin ta yaya za a daidaita batutuwan muhimmin aiki ne da har kullum jam’iyyar da ke kan karagar mulki da ma gwamnatin kasar ke sanyawa a gabansu. A sabili da haka, a karshen kowace shekara, jam’iyyar Kwaminis da ke kan karagar mulkin kasar ta kan kira babban taro kan ayyukan raya yankunan karkara, inda a kan yi nazarin yanayin da ake ciki ta fannonin da suka shafi noma da yankunan karkara da ma manoma, tare da tsara ayyukan da za a gudanar a shekara mai zuwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Daga ranar 17 zuwa 18 ga wata, an gudanar da taron na bana a birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya umarci a gaggauta zamanantar da ayyukan noma da yankunan karkara, da karfafa tushen ayyukan noma, da kara samar da ci gaba mai albarka a yankunan karkara, da kuma kara inganta walwalar manoma, don a cimma burin raya kasar ta zama gagarabadau a fannin ayyukan noma.

 

Noma tushen arzki, kamar dai yadda Hausawa kan ce. Abin hakan yake. A nahiyar Afirka, musamman kasashen da ke kudu da hamadar Sahara, ayyukan noma kan dauki sama da kaso 30% daga cikin jimillar karfin tattalin arziki ta GDP, yayin da sama da kaso 70% na al’ummomin da suke da ayyukan yi suna gudanar da sana’o’i ne da suka shafi noma. Don haka ma, batutuwa masu nasaba da noma da yankunan karkara da kuma manoma su ma suna taka muhimmiyar rawa wurin daidaita matsalolin da kasashen suke fuskanta ta fannonin abinci da saukaka fatara da ma zamanantar da kansu.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kullum kasar Sin na kallon kanta da kasashen Afirka a matsayin al’ummu mai makoma ta bai-daya, abin da ya sa take kokarin raba dabarunta da ma damammakinta ga kasashen Afirka a lokacin da take bunkasa kanta ta fannonin noma da yankunan karkara da ma manoma. A ‘yan shekarun baya, hadin gwiwar ayyukan noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya inganta bisa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da ma tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, tuni har kasar Sin ta kafa cibiyoyin nune-nunen fasahohin noma 24 a kasashen Afirka, tare da yayata fasahohin noma na zamanin fiye da 300, matakan da suka sa amfanin gonar da aka samar a yankunan da abin ya shafa suka karu da kaso 30% zuwa 60%, wadanda kuma suka samar da alfanu ga manoma sama da miliyan a Afirka. “Kasar Sin na taka muhimmiyar rawa a yunkurin kasashen Afirka na zamanantar da ayyukan noma”, in ji Rahamtalla M. Osman, babban wakilin kungiyar tarayyar Afirka a kasar Sin, wanda ya ce, fasahohin da kasar Sin ta samar wa kasashen Afirka sun taimaka wajen tabbatar da dauwamammen ci gaban ayyukan noma a kasashen Afirka, a yayin da kuma suka taimaka ga kara kudin shigar manoma.

 

A gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a watan Satumban bana a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu matakai 10 na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka wajen zamanantar da kansu, ciki har da matakin da ya shafi bunkasa ayyukan noma, wato za a samar da gudummawar hatsi na kimanin kudin Sin yuan biliyan daya ga kasashen Afirka cikin gaggawa, da kafa yankunan nune-nunen fasahohin noma da tura masanan ayyukan noma 500 zuwa kasashen Afirka da kafa kawancen kirkire-kirkiren fasahohin noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka da dai sauransu.

 

Kasancewarsu kawayen juna, kasar Sin za ta rika raba cin gajiyar nasarorinta ga aminanta na Afirka wajen zamanantar da ayyukan noma, don su cimma burinsu na zamanantar da kansu. (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ake Alfahari Da Su (2): Darasi Daga Zuhudun Manzon Allah (SAW)

Next Post

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

16 hours ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

18 hours ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

3 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

3 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

4 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.