• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

Rikice-rikicen da ke da alaka da ayyukan kungiyoyin asiri yana haifar da babban kalubale ga harkar tsaro a makarantu, al’ummomi da harkokin kasuwanci, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, ciki har da wani babban jami’in ‘yansanda dake aiki a yankin Niger Delta.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa tashe-tashen hankulan galibi sun shafi jihohin Kudancin Nijeriya ne, kuma suna lakume rayukan al’umma, sannan a wasu lokutan ya kan tilasta wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro janyewa daga bakin aiki.

  • NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf
  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19

Hakan dai na faruwa ne duk da irin namijin kokarin da ‘yan sandan ke yi na ganin an dakile lamarin, inda aka kama mutane da dama a ‘yan kwanakin nan.

Kuma bisa ga bayanan ‘yansanda da al’ummomi mazauna yankunan, rikicin da ke da alaka da kungiyoyin asiri ya zama ruwan dare, shirye-shiryen ‘yan daba na shiga aikata laifuka yana da alaka da ta’ammali da muggan kwayoyi. Abin da ya fi tsoratarwa shi ne yadda ’yan dabar suka samu hanyar shiga cikin makarantun sakandire a wasu jihohin inda hukumomi suka kasa tabuka komai.

A Akwa Ibom, al’amuran da suka shafi kungiyoyin asiri da matasa masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ke kara ta’azzara tsawon shekaru, wanda a cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), SP Odiko MacDon, shi ne babban dalilin kafa Kungiyar Anti-Cult (ACU) don yakar wannan muguwar dabi’a.

Rikicin da LEADERSHIP Sunday ta gano, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a jihar cikin shekara guda da ta wuce.

“Laifukan da aka samu a jihar da dama na da nasaba da kungiyar asiri kuma da yawa daga cikinsu (‘yan kungiyar asirin) suna tsare, yayin da wasu da dama ke fuskantar shari’o’i daban-daban a kotu, wadanda aka samu da laifi an daure su a gidan yari daban-daban, wasu daga cikinsu ma hukuncin kisa,” wani babban jami’in shigar da kara na hukumar binciken manyan laifuka (CID) da ke Ikot Akpanabia, shedikwatar jihar, ya shaida wa wakilinmu kan sharadin boye sunansa.

Ya ambaci sunan wani Akaniyene Isaac, mai shekaru 23, wanda ya kashe mahaifiyarsa mai shekaru 55 kwanan nan saboda ta ki ba shi kudi domin shan muggan kwayoyi da kuma biyansa wasu bukatu na kashin kansa, a halin yanzu yana fuskantar shari’a a kotu.

“Babban rikicin kungiyar asiri yana faru ne a makarantar Technical Ewet, Garuruwa Hudu da sauransu, inda hakan ya tilasta wa gwamnati shiga tsakani ta hanyar ba da umarnin kafa shingaye, tare da dakatar da wasu dalibai masu laifi, yayin da aka bukaci wasu su zo tare da iyayensu don sanya hannu kan wani aiki kafin su ci gaba da karatunsu.

Bayan haka, ma’aikatar ilimi karkashin jagorancin Kwamishina, Misis Idongesit Etiebet, ta samu ta haramta daukar dalibai ba tare da an shiga kakar karatu ba, a cewar Mis Agnes Thompson, wata malamar makarantar gwamnati a makarantar gwamnati, Iba Oku, “dubi dai yadda ake samun kwararowar dalibai da aka kore su daga wasu makarantu saboda halin daba da kuma yadda suke sake shiga wasu makarantun”.

A jami’ar Uyo (UNIUYO), wani jami’in tsaro Ime Edet ya bayyana cewa jami’o’in biyu da ke titin Ikpa da kuma babbar makarantar da ke Nwaniba, Uyo wanda a da ta kasance gidajen wasan kwaikwayo da ake fama da rikicin addini a tsawon shekaru, a cikin shekara daya da ta wuce, amma ta dawo hayyacinta saboda “ingartacciyar kulawa da saka hannun jari da kula da harkokin tsaro da ‘yan sanda suka yi, da hadin gwiwar hukumar gudanarwar makarantar karkashin jagorancin mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Nyaudoh Ndaeyo.”

Amma a Jami’ar Jihar Akwa Ibom (AKSU), musamman babbar jami’ar da ke Ikot Akpaden da ke Karamar Hukumar Mkpat Enin, an samu kashe-kashen kungiyoyin asiri kamar yadda LEADERSHIP Sunday ta tabbatar, hakan kuma ya sanya tsoro a zukatan dalibai tare da samun wasu kashe-kashen shekarar karatu ta karshe a makarantun ilimi,har ma da cikin al’umma musamman a Kananan Hukumomin Ahoada- Gabas, Ahoada-West da kuma Birnin Fatakwal na jihar.

Wadannan ayyuka, LEADERSHIP Lahadi ta gano cewa, suna tsakanin gungun kungiyoyin asiri na Iceland da ke zaune cikin al’ummomi. Bugu da kari ayyukan wadannan kungiyoyi sun yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a jihar, ciki har da tsohon jami’in ‘yansanda na shiyya (DPO) mai kula da sashen ‘yansanda na Ahoada, Bako Angbashim.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Next Post

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Related

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

5 hours ago
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

6 hours ago
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

12 hours ago
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

15 hours ago
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

1 day ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

1 day ago
Next Post
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira

Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira

July 31, 2025
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

July 31, 2025
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

July 31, 2025
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

July 31, 2025
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.