• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Wasu Tagwaye Suka Kirkiri Murhun Dafa Abinci Mai Amfani Da Ruwa Da Fetur

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Yadda Wasu Tagwaye Suka Kirkiri Murhun Dafa Abinci Mai Amfani Da Ruwa Da Fetur
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hassan Muhammad Nawad da Hussaini Muhammad Nawad tagwaye ne haifaffun Jihar Kano ne wanda a halin yanzu suka samu damar shiga cikin baje fasahar kere-kere na duniya da ake tunkaho da shi. Tagwayen masu shekaru 14 a duniya sun kirkiri abun dafa abinci da zai ke amfani da man fetur da ruwa da zai samar da wutan da nau’ikan abinci ke bukata na tsawon sama da awanni biyar a lokaci guda.

Murhun dafa abincin na dauke da injin da ke amfani da baturi da zai sarrafa ruwa da fetur domin bayar da wutan dafa abinci.

  • ‘Yan Sama Jannatin Sin Sun Kammala Aikin Gyara Na’ura A Wajen Kumbo A Karon Farko
  • Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

Da ake zantawa da tagwayen sun shaida cewa sun tsara amfani da kwakwalwarsu wajen hada wani abun da zai zama mai amfani kuma ya taimaki al’umma. A cewarsu, sun sha zama su baje tunani daban-daban kowa ya kawo abun da yake gani za su yi ko za su bada tasu gudunmawar a lokacin da suke zuwa kwanciya don yin barci, inda suke irin wannan tunanin, kuma, iyayensu sun yi matukar mara musu baya da shawarori da kuma tarbiyyar da zai taimakesu wajen cimma burin mafarkinsu tare da dafa wa tunaninsu da kuma kokarin maido musu da abun da suke tunani zuwa ga zahiri.

Hassan ya ce tunanin hada murhun dafa abinci na zamani ya zo musu sama da shekara biyar da suka wuce, a lokacin da suke makarantar Firamare.

“Na yi ta tunanin ta yaya ake amfani da iskar gas wajen bayar da wutan da ake dafa abinci, sannan, da tunanin yin wani abu da zai kawo sauki kan amfani wutar lantarki domin samar da wutar ta hanyar amfani da ruwa da fetur. Daga nan ne muka fara kama-kama har muka kawo wannan lokacin a yau.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

“Amma, a wannan yanayin, fetur da ruwa ba za su rage wahalar da ake sha. Litar mai zai dauki watanni ba tare da raguwa ba. Kawai za ka canza ne idan ka fahimci ya koma baki da zai dauki kusan shekara 1 kafin yin hakan. Batiri da karamin injin da aka hada za su taimaka wa ruwa da fetur din ne wajen bulbula iskar da zai samar da iska mai konewa da zai bayar da daidai wutar da ake bukata domin dafa abinci,” ya shaida.

Shi ma Hussaini wanda ya yi bayani da cewa, “Shi wannan ruwan da ake hadawa ba zallar ruwa ne ba, ana hadawa ne da alum da kuma gishiri. A cikin akwatin, za ka iya ganin akwai karamin inji da zai ke bayar da iskar da ruwan da fetur za su ke motsawa.”

Hussaini ya kara da cewa, lura da halin matsatsin tattalin arziki da ake fuskanta a fadin kasar nan, don haka ne suka yi tunanin nemo wasu hanyoyin da za su taimaka wajen rage wa jama’a kuncin da ake ciki da kuma bayar da nasu gudunmawar wajen cigaban tattalin arzikin kasar nan.

“Muna son mu kawo wani gagarumin sauyi a cikin matasan arewacin kasar nan. Mun iya fahimtar cewa an bar matasa a bayan baya, kuma fa muna da basira da fikira sosai. Kawai abun da muke nema shi ne wadatar da za mu samu da zai ba mu damar kirkirar ayyukan yi da kuma samar da ababen bukata da saukaka wa al’umma harkokin rayuwa.”

Duk da cewa har yanzu suna makaranta, wanda suke matakin aji SS2 na sakandari, Hassan ya shaida cewar shi da dan uwansa Hussaini sun kuma kirkiri injin feshi mai amfani da cajin wutar lantarki wanda za a yi amfani da shi wajen feshi domin kashe kwari koda kuwa a cikin ruwa suke.

Ya ce, abun feshin zai ke amfani da batirin da za a ke masa cajin wuta ne. Kuma, zai iya aiki na tsawon kwanaki 10 idan aka cikasa da caji.

“Idan ka samu kayan da kake son yin feshi, kawai abun da kake bukata shi ne za a ka yi cajin abun feshinka ka cigaba da amfani da shi. Kuma wannan abun gwanin ban sha’awa kuma zai yi amfani matuka. Shi ne mafi sauki a cikin dukkanin abubuwan da muka hada.”

Tagwayen suka ce, bayan samun nasarar hada murhun dafa abinci da kuma abun feshin maganin kashe kwari, yanzu haka sun dukufa yin aikin su da ke gabansu, wanda a cewarsu shi ne za su hada batiri wanda zai yi aiki wajen bai wa na’urar sanyaya daki ko wuri (AC) kuzarin da yake bukata domin ba sai da wuta ba kafin ya yi amfani a gidajen mutane.

A cewarsu, wannan batiri zai ke bai wa AC abun da yake nema, kuma koda babu wuta AC zai yi aiki da wannan batirin.

“Aikin da muke son yi a nan gaba shi ne na hada Batiri, kuma mun riga ma har mun fara. Baturi ne mai karfin lantarki 12 da zai bai wa AC kuzarin da yake nema da zai bai wa fankoki, firiza, talabijin da sauran abubuwan amfani damar yin aiki a gidaje. Babban aiki ne sosai da muka dunfara amma muna da kwarin guiwar za mu iya kuma za mu yi. Amma a halin yanzu, muna fuskantar wasu ‘yan matsaloli. Wasu daga cikin abubuwan aiki da muke bukata wajen cimma burinmu babu su amma dole mu tsaya har zuwa lokacin da za mu sameshi,” suka shaida.

Baya ga hakan, sun shaida cewar suna da shirye-shiryen kirkirar wasu abubuwa sosai da za su taimaka wajen yin amfani da su a cikin al’umma, sun kara da cewa suna matukar damuwa da yadda jama’a suke shan wahalar gudanar da harkokin rayuwa musamman talakawa, don haka suka dukufa wajen amfani da basirar da Allah ya basu domin kawo sauki da nemo hanyoyin rage matsaloli ga jama’a.

Da suke magana kan muradinsu da fatansu a nan gaba, tagwayen sun ce, suna da burin karanta ilimin fasaha da kwasa-kwasan da suke da alaka da hakan a jami’a da zarar suka kammala karatun sakandari kuma burinsu a wannan gabar shi ne su tafi kasar Turai ko wata kasar da ta cigaba domin samun karin sani, ilimi, gogewa da horon da za su cigaba da cimma burinsu na rayuwa musamman a bangaren kere-kere.

“Muna da manya-manyan shirye-shirye da buri a nan gaba, za mu cigaba da kirkirar abubuwa sosai. Dangane da murhun dafa abinci, za mu sabunta shi mu zamanantar da shi da kara masa kwari. Kuma za mu kirkiri wani da zai ke kasance na da wurin bada wuta da iskar dafa abinci mai wuri biyar ko ma shida domin amfani da shi a gidajen da suke da yawa ko wajajen taruka.

“Babban abun da muke bukata yanzu shi ne goyon baya, gudunmawa da bibiyar da zai kara wa yunkurin azama da kumaji. Muna da muradi a kan abubuwa daban-daban da suka shafi kimiyya. Kuma, mun kasance masu bibiya da kallon matasa irinmu ko ma wadanda suke kasa da mu domin amfani da baiwar da Allah ya musu, a kasashen da suka cigaba. Muna son mu je irin wadannan wuraren domin samun karin horo,” Hussaini ya shaida.

Kazalika, ma ‘yan biyun sun yi kira ga matasa da su shigo a dama da su a harkokin kirkire-kirkire tare da amfani da harkokin fasaha. Sun ce, idan aka yi la’akari da tawakarorinsu da suke wasu kasashe da yadda suke iya amfanar da al’ummarsu, akwai bukatar matasan Nijeriya su shigo a dama da su wajen karawa da takwarorinsu na kasashen waje.

“A duk lokacin da muka ga wani matashi a bangaren fasaha na bada gudunmawarsa a wata kasa, muna samun kwarin guiwa matuka. Muna son mu ga an samu sauyi a wannan bangaren a Afrika. Amma kalubalen da muke fusanta suna da matukar yawa.

“Wasu lokutan ba mu da kayan aiki da muke bukata. Za mu tsara mu jira ko kuma mu watsar da aikin da muka sanya a gaba ko muka fara. Amma muna da yakin gwamnatocinmu za su shigo su taimaka wa matasan da suke da basira domin a amfani baiwar da Allah ya musu. Ta wannan hanyar za mu yaki matsalar rashin ayyukan yi da talauci a tsakanin matasa da ma al’umma.”

Tagwayen sun kuma bukaci matasa da su yi koyi da abun da suke yi wajen ganin sun taimaka wa al’umma. Sannan, sun gode da jinjina wa cibiyar bunkasa fasahar sadarwa wato (CITAD) bisa tallafin da take basu na kayan aiki da kuma nema musu damar samun zuwa dakunan gwaje-gwaje na fasaha daban-daban kan ayyukansu da suke yi.

“CITAD ta taimakemu da wasu kayayyaki da kayan aiki da dama. Kuma sun taimaka mana da samun damar wuraren kara wa juna sani da dama, inda muke zuwa a kowani rana domin yin ayyukanmu. Wannan a zahiri ya taimaka mana matuka da karfafa mana guiwa wajen cimma manufofin da muka sanya a gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hauhawar Farashin Dala: Ina Mafita Ga Nijeriya?

Next Post

Jan Kunne Ga Uwargida

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

2 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

3 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

3 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

4 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

8 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

8 months ago
Next Post
Jan Kunne Ga Uwargida

Jan Kunne Ga Uwargida

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.