• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Ma’aikata Hudu Da ‘Yansanda Biyu A Kamfanin Sarrafa Tasa

by Ahmed Muhammed Danasabe
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 36 A Wani Sabon Hari A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga da ba a san kosu wane ne ba sun kai mummunar hari a kamfanin sarrafa tasa da ke Ajaokuta a Jihar Kogi, inda suka hallaka mutum shida da suka hada da ma’aikata ‘yan kasashen waje biyu da direbobin kamfanin biyu da kuma jami’an ‘yansanda biyu tare da garkuwa da ma’aikata uku ‘yan kasashen waje da ke aiki a kamfanin. 

Harin ya zo ne bayan makonni biyu da wasu ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Jida Bassa da ke yankin karamar hukumar ta Ajaokuta, inda suka hallaka ‘yan sanda uku da ‘yan sintiri (bijilante) biyar da kuma sace yara uku a rukunin gidaje na Kaduna da ke kamfanin sarrafa karafa na Ajaokuta, inda suka nemi a biya su kudin fansa har naira miliyan dari kafin su saki kananan yaran uku wadda shekarunsu suka kama daga biyar, bakwai zuwa goma.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • Dariye Zai Tsaya Takarar Sanata A Filato Bayan Yi Masa Afuwa Daga Gidan Yari

Wata majiya ta shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa cewa ‘yan bindigan sun shigo kamfanin sarrafa tasan da ke karamar hukumar Ajaokuta na Jihar Kogi ne da misalin karfe bakwai na daren ranar Juma’ar da ta gabata, inda suka kashe ma’aikatan kamfanin hudu da ke cikin motar bas da ke shirin kai su wurare dabam-dabam.

Wani ganau wanda ya nemi a sakaye sunansa ya ce ‘yan bindigan wadanda suka kawo harin cikin motoci biyu, sun yi wa ma’aikata ‘yan kasashen wajen da sauran ma’aikatan dak e cikin motar kamfanin kwantar bauna, inda suka fara harbin kan mai-uwada-wabi.

Ya ce, “Yau wata ranan bakin ciki ne garemu a nan Ajaokuta, muna cikin jimamin kashe jami’an tsaro bakwai da ‘yan bindiga suka yi a Jida Bassa kwanan nan da yin garkuwa da yara uku duk a nan Ajaokuta, sai gashi kuma wannan ya auku, to yaya za mu yi da rayukannu?

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

“Wadanda suka rasa rayukansu da wadanda ‘yan bindigan suka yi garkuwa da su suna shirin barin kamfanin ne zuwa masaukinsu da ke rukunun gidaje na Neja da ke Ajaokutan kafin ‘yan bindigan su yi musu kwantar bauna.

Ya ce, “Suna aiki ne a kamfanin sarrafa tasa na yammacin Afirka da ke nan Ajaokuta.

“Jami’an ‘yan sanda sun rika musayar wuta da bata-garin, amma abin takaici biyu daga cikin ‘yan sandan da direbobin kamfanin guda biyu da kuma ma’aikata ‘yan kasashen waje, sun rasa rayukansu a cikin motar kamfanin, a yayin da kuma ‘yan bindigan suka yi garkuwa da ma’aikata ‘yan kasashen waje uku,” in ji shi.

A bangare guda kuma, kwamishinan watsa labarai na Jihar Kogi, Mista Kingsley Fanwo, a martanin da yayi game da harin ya ce gwamnatin jihar ta yi Allah wadai da wannan harin.

Ya kuma kara da cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ceto wadanda aka yi garkuwa da su da kuma zakulo wadanda suka aikata wannan mummunar aiki.

Kwamishinan ya kuma ce wannan hari da sauran ayyukan bata-gari ko kadan ba zai karya wa gwambatin Jihar Kogi karkashin shugabancin Gwamna Yahaya Bello wajen kare lafiya da kuma dujiyoyin al’umma, sannan ya gargadi masu aikata laifufuka da su gaggauta sauya wani wurin don aikata laifi.

Haka shi ma kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kogi, CP Edward Egbuka, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kogi, Mista William Aya a wata sanarwa da ya fitar, ya ce rundunar ta fara bincike game da faruwar lamarin kuma a shirye take ta zakulo wadanda suka aikata danyen aikin.

Kawo hada wannan labarin, ‘yan bindigan ba su tuntubi iyalai ko kamfanin sarrafa tasan ba domin amsar kudin fansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmakiGarkuwaHarbiHariKamfaniMa'aikataTasaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Next Post

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

4 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

5 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

6 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

7 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

9 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

10 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.