• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Wata mai yi wa kasa hidima (NYSC) wacce take aikin hidimar kasa a karamar hukumar Gamawa da ke jihar Bauchi, Khadija Lukman ta gwangwaje mutane masu fama da lalura ta musamman a karamar hukumar da Kekunan Hawa guda 100 domin saukaka musu gudanar da harkokin rayuwa. 

Khadija mai lambar shaidar hidimar kasa BA/23A/3158 ta bayyana a wajen bikin mika kekunan hawan a ranar Juma’a cewa, wannan wani mataki ne na cika alkawarin da ta yi na cewa za ta taimaka wa masu fama da bukata ta musamman tun lokacin da take makaranta.

  • Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji
  • Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

A cewar jarumar matashiyar, wannan tallafin nata ta bayar ne ba wai domin ta karfafa wa wadanda suka ci gajiyar kekunan cigaba da yin barace-barace ba, illa domin ta taimakesu da karfafa musu guiwa wajen zirga-zirgan neman inganta rayuwarsu.

Khadija ta jawo hankalin wadanda suka ci gajiyar da kar su yi kasa a guiwa ko cire tsammani wajen fafutukar cika burikan rayuwarsu a kowani lokaci.

Khadija ta ce ta samu tallafi wajen aiwatar da wannan kyakkyawar aikin nata ne da gudunmawar daraktan cibiyar Beautiful Gate Handicap da ke Jos ta jihar Filato, Barista Ayuba Gufwan.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

A gefe guda, mambar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima, ta kuma horas da matasa sama da 100 kan yadda za su hada sabulu, man shafawa, kamshin daki da dai sauransu.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar, Fatima Muhammad, ta gode wa ‘yar Hidimar kasar da wanda ya dauki nauyin tallafin bisa taimaka musu, ta musu addu’ar Allah saka musu da alkairi.

A bangarenta, ko’odinetar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) a jihar Bauchi, Rifkatu Yakubu, ta jinjina wa matashiyar ne bisa gudanar aikin da kai tsaye zai kawo sauki ga mutane masu fama da bukata ta musamman.

Kan hakan ne ta yi kira ga masu hannu da shuni da gwamnatoci da su karfafawa matasa masu yi wa kasa hidima da ke da kyakkyawar niyya da tsarin da za su taimakawa al’umma a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi
Labarai

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
Labarai

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Next Post
Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.