• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata mai yi wa kasa hidima (NYSC) wacce take aikin hidimar kasa a karamar hukumar Gamawa da ke jihar Bauchi, Khadija Lukman ta gwangwaje mutane masu fama da lalura ta musamman a karamar hukumar da Kekunan Hawa guda 100 domin saukaka musu gudanar da harkokin rayuwa. 

Khadija mai lambar shaidar hidimar kasa BA/23A/3158 ta bayyana a wajen bikin mika kekunan hawan a ranar Juma’a cewa, wannan wani mataki ne na cika alkawarin da ta yi na cewa za ta taimaka wa masu fama da bukata ta musamman tun lokacin da take makaranta.

  • Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji
  • Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

A cewar jarumar matashiyar, wannan tallafin nata ta bayar ne ba wai domin ta karfafa wa wadanda suka ci gajiyar kekunan cigaba da yin barace-barace ba, illa domin ta taimakesu da karfafa musu guiwa wajen zirga-zirgan neman inganta rayuwarsu.

Khadija ta jawo hankalin wadanda suka ci gajiyar da kar su yi kasa a guiwa ko cire tsammani wajen fafutukar cika burikan rayuwarsu a kowani lokaci.

Khadija ta ce ta samu tallafi wajen aiwatar da wannan kyakkyawar aikin nata ne da gudunmawar daraktan cibiyar Beautiful Gate Handicap da ke Jos ta jihar Filato, Barista Ayuba Gufwan.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

A gefe guda, mambar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima, ta kuma horas da matasa sama da 100 kan yadda za su hada sabulu, man shafawa, kamshin daki da dai sauransu.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar, Fatima Muhammad, ta gode wa ‘yar Hidimar kasar da wanda ya dauki nauyin tallafin bisa taimaka musu, ta musu addu’ar Allah saka musu da alkairi.

A bangarenta, ko’odinetar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) a jihar Bauchi, Rifkatu Yakubu, ta jinjina wa matashiyar ne bisa gudanar aikin da kai tsaye zai kawo sauki ga mutane masu fama da bukata ta musamman.

Kan hakan ne ta yi kira ga masu hannu da shuni da gwamnatoci da su karfafawa matasa masu yi wa kasa hidima da ke da kyakkyawar niyya da tsarin da za su taimakawa al’umma a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kyautata rayuwar matasaMasu Bukata Ta MusammanMasu Yi Wa Kasa Hidima
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin: Ya Zama Wajibi A Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Next Post

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

1 hour ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

19 hours ago
Next Post
Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.