• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata mai yi wa kasa hidima (NYSC) wacce take aikin hidimar kasa a karamar hukumar Gamawa da ke jihar Bauchi, Khadija Lukman ta gwangwaje mutane masu fama da lalura ta musamman a karamar hukumar da Kekunan Hawa guda 100 domin saukaka musu gudanar da harkokin rayuwa. 

Khadija mai lambar shaidar hidimar kasa BA/23A/3158 ta bayyana a wajen bikin mika kekunan hawan a ranar Juma’a cewa, wannan wani mataki ne na cika alkawarin da ta yi na cewa za ta taimaka wa masu fama da bukata ta musamman tun lokacin da take makaranta.

  • Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji
  • Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

A cewar jarumar matashiyar, wannan tallafin nata ta bayar ne ba wai domin ta karfafa wa wadanda suka ci gajiyar kekunan cigaba da yin barace-barace ba, illa domin ta taimakesu da karfafa musu guiwa wajen zirga-zirgan neman inganta rayuwarsu.

Khadija ta jawo hankalin wadanda suka ci gajiyar da kar su yi kasa a guiwa ko cire tsammani wajen fafutukar cika burikan rayuwarsu a kowani lokaci.

Khadija ta ce ta samu tallafi wajen aiwatar da wannan kyakkyawar aikin nata ne da gudunmawar daraktan cibiyar Beautiful Gate Handicap da ke Jos ta jihar Filato, Barista Ayuba Gufwan.

Labarai Masu Nasaba

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

A gefe guda, mambar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima, ta kuma horas da matasa sama da 100 kan yadda za su hada sabulu, man shafawa, kamshin daki da dai sauransu.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar, Fatima Muhammad, ta gode wa ‘yar Hidimar kasar da wanda ya dauki nauyin tallafin bisa taimaka musu, ta musu addu’ar Allah saka musu da alkairi.

A bangarenta, ko’odinetar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) a jihar Bauchi, Rifkatu Yakubu, ta jinjina wa matashiyar ne bisa gudanar aikin da kai tsaye zai kawo sauki ga mutane masu fama da bukata ta musamman.

Kan hakan ne ta yi kira ga masu hannu da shuni da gwamnatoci da su karfafawa matasa masu yi wa kasa hidima da ke da kyakkyawar niyya da tsarin da za su taimakawa al’umma a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kyautata rayuwar matasaMasu Bukata Ta MusammanMasu Yi Wa Kasa Hidima
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin: Ya Zama Wajibi A Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Next Post

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

Related

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

9 minutes ago
Bauchi
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

3 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

3 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

4 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

4 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

5 hours ago
Next Post
Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

LABARAI MASU NASABA

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Bauchi

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Bauchi

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.