• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yunwa Da Kunci Suka Karu Bayan Fara Azumin Ramadan A Gaza

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Yadda Yunwa Da Kunci Suka Karu Bayan Fara Azumin Ramadan A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Falasdinu sun fara gudanar da azumin watan Ramadan cikin halin kunci, daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawar tsagaita wuta, inda yunwa ke kara ta’azzara a yankin Zirin Gaza yayin da har yanzu aka kasa kawo karshen yakin da Isra’ila ta kwashe watanni biyar tana yi a kan fararen hula.

“Wannan wata na Ramadan ya sha bamban da dukkan Ramadan da suka gabata,” in ji Bilal abed Rabbo mazaunin Ramallah.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1
  • NEDC Ta Rarraba Kayayyakin Noman Rani A Jihar Yobe

A taron majalisar ministocin kasar na mako-mako, Firaministan Falasdinu Mohammed Shtayyeh, ya bayyana cewa, “Watan Ramadan ya zo a wannan shekara, yayin da al’ummarmu a Zirin Gaza ke fama da yunwa da kisa sakamakon laifukan kisan kiyashi da ake ci gaba da yi ba tare da kakkautawa ba, muna sa ran shiga tsakani.”

Ya ce suna jiran kotun duniya ta dakatar da wadannan munanan laifuka, sannan suna rokon Allah ya sanya ranakun watan nan mai alfarma ya kasance sassauci ga wadanda suke cikin ukuba, kuma a daina zubar da jini, yana mai kara cewa, Allah ne kadai yake da ikon ceto wadanda suke cikin yunwa da kuma rashin lafiya.

Falasdinawa dai na ganin cewa za a samu tashin hankali daga Yahudawan da ke kyamar Musulunci a cikin watan Ramadan.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

“Na yi imanin cewa ayyukan shahada za su karu kuma tsayin daka zai karu, musamman ta fuskar al’amarin Aqsa da hana masu ibada shiga masallacin domin yin addu’a, musamman matasa,” in ji Jamal mazaunin Ramallah.

Kasashen Qatar, Masar da Amurka sun yi fatan kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta a daidai lokacin da ake gudanar da azumin Ramadan, wanda zai hada da sakin dimbin Yahudawan da aka yi garkuwa da su da kuma fursunonin Falasdinu, hadi da bude hanyoyin shigar da kayayyakin jin-kai, amma tattaunawar ta ci tura a makon jiya.

Hamas dai na neman a ba da tabbacin cewa wannan yarjejeniya za ta kai ga kawo karshen yakin, yayin da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sha alwashin ci gaba da kai hare-hare har zuwa lokacin da zai kawar da Hamas din da kuma kwato sauran Yahudawan da ke hannun kungiyar.

Yakin ya kori kusan kashi 80 na al’ummar Gaza mai mutane miliyan 2.3 daga gidajensu tare da jefa dubbai cikin matsananciyar yunwa.

Jami’an lafiya sun ce akalla mutane 20 galibi yara kanana ne suka mutu sakamakon rashin abinci mai gina jiki da kuma rashin ruwa a Arewacin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun rufe arewacin kasar tun daga watan Oktoban 2023, kuma kungiyoyin agaji sun ce takunkumin da Isra’ila ke ci gaba da kakabawa yankin da tabarbarewar doka da oda, sun sun hana isar da isasshen abinci zuwa Gaza.

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta sanar da cewa akalla Falasdinawa 31,112 aka kashe tun bayan fara yakin, ciki har da gawarwaki 67 da aka kai asibitoci cikin sa’o’i 48 da suka gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuIsra'ilaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Da IBB Sun Yi Ganawar Sirri A Neja

Next Post

Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi – Sufeton ‘Yansanda

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

7 hours ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

1 day ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

6 days ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi – Sufeton ‘Yansanda

Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.