• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yunwa Da Kunci Suka Karu Bayan Fara Azumin Ramadan A Gaza

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Yadda Yunwa Da Kunci Suka Karu Bayan Fara Azumin Ramadan A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Falasdinu sun fara gudanar da azumin watan Ramadan cikin halin kunci, daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawar tsagaita wuta, inda yunwa ke kara ta’azzara a yankin Zirin Gaza yayin da har yanzu aka kasa kawo karshen yakin da Isra’ila ta kwashe watanni biyar tana yi a kan fararen hula.

“Wannan wata na Ramadan ya sha bamban da dukkan Ramadan da suka gabata,” in ji Bilal abed Rabbo mazaunin Ramallah.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1
  • NEDC Ta Rarraba Kayayyakin Noman Rani A Jihar Yobe

A taron majalisar ministocin kasar na mako-mako, Firaministan Falasdinu Mohammed Shtayyeh, ya bayyana cewa, “Watan Ramadan ya zo a wannan shekara, yayin da al’ummarmu a Zirin Gaza ke fama da yunwa da kisa sakamakon laifukan kisan kiyashi da ake ci gaba da yi ba tare da kakkautawa ba, muna sa ran shiga tsakani.”

Ya ce suna jiran kotun duniya ta dakatar da wadannan munanan laifuka, sannan suna rokon Allah ya sanya ranakun watan nan mai alfarma ya kasance sassauci ga wadanda suke cikin ukuba, kuma a daina zubar da jini, yana mai kara cewa, Allah ne kadai yake da ikon ceto wadanda suke cikin yunwa da kuma rashin lafiya.

Falasdinawa dai na ganin cewa za a samu tashin hankali daga Yahudawan da ke kyamar Musulunci a cikin watan Ramadan.

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

“Na yi imanin cewa ayyukan shahada za su karu kuma tsayin daka zai karu, musamman ta fuskar al’amarin Aqsa da hana masu ibada shiga masallacin domin yin addu’a, musamman matasa,” in ji Jamal mazaunin Ramallah.

Kasashen Qatar, Masar da Amurka sun yi fatan kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta a daidai lokacin da ake gudanar da azumin Ramadan, wanda zai hada da sakin dimbin Yahudawan da aka yi garkuwa da su da kuma fursunonin Falasdinu, hadi da bude hanyoyin shigar da kayayyakin jin-kai, amma tattaunawar ta ci tura a makon jiya.

Hamas dai na neman a ba da tabbacin cewa wannan yarjejeniya za ta kai ga kawo karshen yakin, yayin da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sha alwashin ci gaba da kai hare-hare har zuwa lokacin da zai kawar da Hamas din da kuma kwato sauran Yahudawan da ke hannun kungiyar.

Yakin ya kori kusan kashi 80 na al’ummar Gaza mai mutane miliyan 2.3 daga gidajensu tare da jefa dubbai cikin matsananciyar yunwa.

Jami’an lafiya sun ce akalla mutane 20 galibi yara kanana ne suka mutu sakamakon rashin abinci mai gina jiki da kuma rashin ruwa a Arewacin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun rufe arewacin kasar tun daga watan Oktoban 2023, kuma kungiyoyin agaji sun ce takunkumin da Isra’ila ke ci gaba da kakabawa yankin da tabarbarewar doka da oda, sun sun hana isar da isasshen abinci zuwa Gaza.

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta sanar da cewa akalla Falasdinawa 31,112 aka kashe tun bayan fara yakin, ciki har da gawarwaki 67 da aka kai asibitoci cikin sa’o’i 48 da suka gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuIsra'ilaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Da IBB Sun Yi Ganawar Sirri A Neja

Next Post

Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi – Sufeton ‘Yansanda

Related

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

8 hours ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

10 hours ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

22 hours ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

5 days ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

6 days ago
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
Kasashen Ketare

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

1 week ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi – Sufeton ‘Yansanda

Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.