ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yunwa Da Kunci Suka Karu Bayan Fara Azumin Ramadan A Gaza

by Sadiq
2 years ago
Yunwa

Al’ummar Falasdinu sun fara gudanar da azumin watan Ramadan cikin halin kunci, daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawar tsagaita wuta, inda yunwa ke kara ta’azzara a yankin Zirin Gaza yayin da har yanzu aka kasa kawo karshen yakin da Isra’ila ta kwashe watanni biyar tana yi a kan fararen hula.

“Wannan wata na Ramadan ya sha bamban da dukkan Ramadan da suka gabata,” in ji Bilal abed Rabbo mazaunin Ramallah.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1
  • NEDC Ta Rarraba Kayayyakin Noman Rani A Jihar Yobe

A taron majalisar ministocin kasar na mako-mako, Firaministan Falasdinu Mohammed Shtayyeh, ya bayyana cewa, “Watan Ramadan ya zo a wannan shekara, yayin da al’ummarmu a Zirin Gaza ke fama da yunwa da kisa sakamakon laifukan kisan kiyashi da ake ci gaba da yi ba tare da kakkautawa ba, muna sa ran shiga tsakani.”

ADVERTISEMENT

Ya ce suna jiran kotun duniya ta dakatar da wadannan munanan laifuka, sannan suna rokon Allah ya sanya ranakun watan nan mai alfarma ya kasance sassauci ga wadanda suke cikin ukuba, kuma a daina zubar da jini, yana mai kara cewa, Allah ne kadai yake da ikon ceto wadanda suke cikin yunwa da kuma rashin lafiya.

Falasdinawa dai na ganin cewa za a samu tashin hankali daga Yahudawan da ke kyamar Musulunci a cikin watan Ramadan.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

“Na yi imanin cewa ayyukan shahada za su karu kuma tsayin daka zai karu, musamman ta fuskar al’amarin Aqsa da hana masu ibada shiga masallacin domin yin addu’a, musamman matasa,” in ji Jamal mazaunin Ramallah.

Kasashen Qatar, Masar da Amurka sun yi fatan kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta a daidai lokacin da ake gudanar da azumin Ramadan, wanda zai hada da sakin dimbin Yahudawan da aka yi garkuwa da su da kuma fursunonin Falasdinu, hadi da bude hanyoyin shigar da kayayyakin jin-kai, amma tattaunawar ta ci tura a makon jiya.

Hamas dai na neman a ba da tabbacin cewa wannan yarjejeniya za ta kai ga kawo karshen yakin, yayin da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sha alwashin ci gaba da kai hare-hare har zuwa lokacin da zai kawar da Hamas din da kuma kwato sauran Yahudawan da ke hannun kungiyar.

Yakin ya kori kusan kashi 80 na al’ummar Gaza mai mutane miliyan 2.3 daga gidajensu tare da jefa dubbai cikin matsananciyar yunwa.

Jami’an lafiya sun ce akalla mutane 20 galibi yara kanana ne suka mutu sakamakon rashin abinci mai gina jiki da kuma rashin ruwa a Arewacin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun rufe arewacin kasar tun daga watan Oktoban 2023, kuma kungiyoyin agaji sun ce takunkumin da Isra’ila ke ci gaba da kakabawa yankin da tabarbarewar doka da oda, sun sun hana isar da isasshen abinci zuwa Gaza.

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta sanar da cewa akalla Falasdinawa 31,112 aka kashe tun bayan fara yakin, ciki har da gawarwaki 67 da aka kai asibitoci cikin sa’o’i 48 da suka gabata.

MASU ALAKA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
Kasashen Ketare

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
Kasashen Ketare

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi – Sufeton ‘Yansanda

Za Mu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Azumi - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.