• Leadership Hausa
Monday, May 29, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za Ki Zauna Tare Da Surukai Masu Sa Ido

by Rabi'at Sidi Bala
3 months ago
in Taskira
0
Yadda Za Ki Zauna Tare Da Surukai Masu Sa Ido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar kowanne mako wannan shafi ya kan zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma daga bangarori daban-daban. Inda tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da irin sirikai (Iyayen miji) suke saka ido a kan matan ‘ya’yansu maza.

Musamman ta yadda suke ganin yaran nasu na kyautatawa matansu na hakkokin daya rataya a wuyansu, wanda kuma dalilin hakan kan saka iyayen mijin tsanar matan ‘ya’yansu ta yadda za su zamo tamkar kishiyoyinsu, har ta kai ga sirikan sun zama abokan gaba.

Ko me ya ke saka su aikata hakan?, wanne irin matsaloli hakan ke iya haifarwa?, ko ta wacce hanya za a yi kokarin ganar da sirikai masu irin wannan halin?. Dalilin hakan shafin Taskira ya ji ta bakin wasu daga cikin mabiyansa, inda suka bayyana nasu ra’ayoyin kamar haka:

Sunana Abubakar Muhammad Shehu daga Jihar Kano:
Gaskiya hakan ba daidai bane saboda, abin da ya ke yi haki ne a kansa ya zama dole. Abin da ya ke sa su haka, son zuciya ne kuma babu fahimta a tsakanin su. Matsalar da ya ke haifar wa ita ce zai sa ita matar ta daina ganin girman sirikar ta su hakan na iya raba ‘ya’yan da matan, idan ni ne zan yi kokari mu fahimci juna tsakanina da ita kamar janyo mata aya da hadisai da dai sauransu. Shawara ta a nan ita ce ya kamata tayi kokari ta hada kan iyalanta domin hakan raba kan iyalanta ne da jikokinta, ina godiya ina yi muku fatan Alheri.

Sunana mustapha Abdullah Abubakar (daga garin Jos):
Yana daya daga cikin abubuwa mafi girma wajan mutuwar Aure ko da kuwa akwai soyayya mai karfi tsakanin ma’aurata, uwar miji ba ta da wata alaka da abun da danta ya ke siyowa matar sa. Ko da addinin musulunci bai ce dole idan maigida zai yi wa matar sa wata hidima ta rayuwa sai ya fadawa mahaifiyar sa ba. Mafi yawancin irin wannan sirika ko (uwar miji) son zuciya ne kawai domin cimman wata bukatar su ta Rayuwa. Gaskiya akwai matsaloli da dama kamar rashin ganin girman juna, da kuma rabuwar aure duk dalilin sirika masu aikata irin wanna halin. Matakin da zan dauka shi ne; zan kai kukana ga Allah subhanahu wata’ala domin na san shi ne zai biya mun dukkan bukatu na, daga bisani zan yi kokarin kai karar ta wajan malaimai domin tunatar da ita hakkoiki na a wajan mijina, da kuma ita ma nata hakkin a gun mijina. Shawara ta shi ne yana da kyau sirikai (iyayen miji) su rike girmansu, a matsayinsu na manya, kuma abun kwaikwayo ga zamantakewar Aure.

Labarai Masu Nasaba

Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

Tsokaci Kan Maza Masu Boye Bayanan Kansu Wurin Neman Aure

Sunana Habiba Mustapha Abdullahi daga Jihar Kano:
Shawarata anan shi ne gaskiya ire-iren wannan abun ya kan kawo ci baya ga rayuwar ‘ya’yansu, dan Allah kowa ya tsaya a iya matsayisa, muguwar shawara ta kawaye iyayyen miji da yawan zuwa gidan yara, rashin zaman lafiya da mugaye kalamai ka ji ana cewa Allah ya sa ta mutu mu huta da dai soransu, yawan hakuri da rashin maida magana da yawan ambaton Allah, dan allah sirrikai mu ke yawan bawa zuciyar mu hakuri saboda kowa yana da mace kuma idan an yi wa ‘yar ki ba za ki ji dadin haka ba, da Allah mu kula sosai.

Sunana Masa’ud Saleh Dokadawa:
To a gaskiya haka yana faruwa, surukai mata suna sawa matan ‘ya’yansu ido kan duk wata kyautatawa da suke yi masu, da yunkurin hana mazajen yi wa matan abubuwan jindadi. Ba daidai bane kuma su ma sun haifi ‘ya’ya matan, idan aka yi musu ba za su ji dadi ba. Abin da ya sa suke aikata hakan sun hada da; Rashin samun kyautatawa daga ‘ya’yan nasu mazan, Ganin kyashi akan abin da mazan ke wa matansu, Rashin ganin girman surukan da karancin yi musu biyayya, yana sawa suruka ta takurawa matar da, Karancin tausayi da ganin kyashi daga iyayen mijin, Karancin tsoron Allah da ilimin addini. Rashin zaman lafiya a cikin zuria, yawan samun mace-macen aure don iyayen mijin na saka ‘ya’yansu su saki matan ko da ba sa so, yana kawo raini, wulakanci, gaba tsakaninmu ko danginsu duka biyun. Idan ni ce zan yi iya kokarina wajen yi mata biyayya sau da kafa, don samun farin cikin mijina, sannan zan dinga yawan kyautata mata tsakanina da Allah, akwai hadisin Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa “an lullube zukata da son wanda ya kyautata mata, da kin wanda ya munana mata”. Sai kuma yawaita addu’a dare da rana akan Allah ya ganar da ita ta daina, sai nasihohi kadan-kadan. Su ji tsoron Allah su daina don hakan rashin tausayi ne da zalinci, kuma hali ne mara kyau, wanda bai dace da iyaye ba ta ko Ina.

Sunana Fatima Jaafar Abbas daga Rimin Gado LGA:
Gaskiya dai iyayen miji masu saka ido ko kuma su dinga kishi akan abin da miji ya ke wa matarsa hakan ba daidai bane, domin ita dole ce a gare shi ya kiyaye duk wasu hakkokinta kamar yadda Musulunci ya tanada ita kuma mahaifiya ya kyautata mata daidai da shari’a ita ma, don haka kuskure ne sirikai ke yi akan haka. Gaskiya son zuciya ne ya ke sa su suyi haka kuma su in sun kai ‘ya’yansu mata wani gidan za su so a kyautata musu. Hakan na janyo manyan matsaloli daga ciki yana sa har ayi (SAKI) yana kuma janyo raini ita yarinyar ta raina uwar mijin daga nan kuma sai matsaloli su yi ta yawa. Idan ni ce matakin da zan dauka shi ne; zan yi hakura a mataki na farko in yi Mata uziri in kuma dinga kyautata mata ta wannan hanyar ne zan samu in janyo hankalinta don ta daina. Iyayen mijin su ji tsoron Allah ita ma matar ta dinga kyautata wa mahaifiyar mijinta don ita ma mahaifiyar ta ce.

Sunana Zulkifilu Lawal (NAKA SAI NAKA):
Uwar miji wadda take sa ido akan abin da danta ya ke yi wa matarsa gaskiya bai kamata ba, ya kamata uwar miji ta sani ita ma matar tana da iyaye kuma tana sonsu, amman soyayyar da take yi wa danta ya sa ta zabi zama da shi, ta rabu da nata iyayen. Bai kamata uwar miji tana kishi da matar danta ba saboda wata hidima daya ke yi mata ba, yin hakan ya kan iya haifar da raini a tsakaninsu, mataki shi ne sai an kara hakuri da juriya da kai zuciya nesa da karantar halayen surikan, ya kamata surikai su sani matan ‘ya’yansu ba kishiyoyinsu bane, Allah ya sa mu dace.

Sunana Fadila Lamido daga Jihar Kaduna:
Allah ya shiryeta ta daina saka idon, domin ita ya kamata ta dinga daura danta a hanya, tana nuna mishi yadda zai kula da matarshi. Matar danki ai ba kishiyarki ba ce, abin da ya ke kawo hakan a tunanina son zuciya ne zai sa ta kasa daukar matar yaron a matsayin ‘yarta, in da ta dauketa ‘yarta kamar yadda mijin ya ke danta ba za ta yi kishi da ita ba, domin ta san matsayinta ya zarce na mata, ita uwa ce gaba daya. Kuma in da ace tana da yariya mace ba za ta so uwar mijinta ta sa mata ido ba, saboda wannan ‘yar ta ce ta san ciwonta. Matsalar da hakan ya ke jawowa na farko raini zai shiga tsakaninki da matar danki, domin duk ranar da ta fahimci kishi kike da ita za ta raina ki, daga baya kuma kiyayyarki za ta shiga zuciyarta, ke kina jin haushinta ita ma, tanajin haushinki, dan za ta dinga ganin kin takura mata, matsayinki daban, nata daban. Kuma a matsayin ki na uwa ya dace tun kafin danki yayi aure ki tarbiyantar da shi kulawa da ke, ya zamar masa jiki ta yadda idan yayi aure sai dai ki dinga kara karfafa mishi guiwa wajen sauke nauyin dake kanshi. Idan ni ce na samu uwar miji irin wannan, matakin da zan dauka shi ne; ba zan dinga bari ta san motsina ba, zan ja hankalin mijina ya suturta siyayyata, ya bayyana nata, tare da yi mata hidima a bayyane, hakan zai sa ta ji ta gamsu ta bar mu mu zauna lafiya, domin wani lokacin mai hali baya canza halinshi.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kauran Bauchi Zai Gyara Kasuwar Katako Da Gobara Ta Kone Da Tallafin Miliyan 10

Next Post

Wakiliyar CGTN Ta Zanta Da Mai Tono Asiri Game Da Bututun Iskar Gas Na Nord Stream

Related

Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu
Taskira

Dabi’ar Wasu Maza Ta Kiran ‘Yan Mata A Waya A Gaban Matansu

1 week ago
Tsokaci Kan Maza Masu Boye Bayanan Kansu Wurin Neman Aure
Taskira

Tsokaci Kan Maza Masu Boye Bayanan Kansu Wurin Neman Aure

2 weeks ago
Tsakanin Mace Mai Bala’in Son Kudi Da Mai Yawo, Da Namiji Mai Kulle Ko Mako, Wanne Ne Dama-dama?
Taskira

Tsakanin Mace Mai Bala’in Son Kudi Da Mai Yawo, Da Namiji Mai Kulle Ko Mako, Wanne Ne Dama-dama?

3 weeks ago
Dubi Ga Batun Cewa, ‘Ba A Yin Budurwa Ranar Sallah’
Taskira

Dubi Ga Batun Cewa, ‘Ba A Yin Budurwa Ranar Sallah’

4 weeks ago
Tsokaci A Kan Sabanin Da Ake Samu Wurin Mu’amala
Taskira

Tsokaci A Kan Sabanin Da Ake Samu Wurin Mu’amala

2 months ago
Tsokaci A Kan Baje Kolin Matan Aure A Shafukan Intanet
Taskira

Tsokaci A Kan Baje Kolin Matan Aure A Shafukan Intanet

3 months ago
Next Post
Wakiliyar CGTN Ta Zanta Da Mai Tono Asiri Game Da Bututun Iskar Gas Na Nord Stream

Wakiliyar CGTN Ta Zanta Da Mai Tono Asiri Game Da Bututun Iskar Gas Na Nord Stream

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

May 29, 2023
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

May 29, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

May 29, 2023
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

May 29, 2023
Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

May 29, 2023
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

May 29, 2023
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

May 28, 2023
An Wallafa Littafin Dake Kunshe Da Mukalolin Shugaba Xi Kan Dogaro Da Kai A Fannin Kimiyya Da Fasaha

An Wallafa Littafin Dake Kunshe Da Mukalolin Shugaba Xi Kan Dogaro Da Kai A Fannin Kimiyya Da Fasaha

May 28, 2023
Ganduje Yayi Jawabin Bankwana Tare Da Shirin Mika Mulki A Yau Lahadi

Ganduje Yayi Jawabin Bankwana Tare Da Shirin Mika Mulki A Yau Lahadi

May 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.