ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

by Rabi'at Sidi Bala and Sulaiman
1 year ago
Mata

Shafin TASKIRA shafi ne daya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, ciki sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya da dai sauransu.

Tsokacin mu yau zai yi duba ne game da abin da ya shafi musgunawa ‘ya’ya wanda iyaye mata ke yi. Wasu daga cikin iyaye mata suna gallaza wa ‘ya’yansu na cikinsu, don ganin sun bakantawa mazajensu rai musamman idan suka samu sabani da juna, ko ya hana wani abun wanda ba sa so a hana su.

Dalilin hakan ya sa muka ji ta bakin wasu daga cikin mabiya shafin game da wannan batun “Me za a ce a kan hakan?, wane amfani yin hakan yake da shi?, ko akwai wata matsala da hakan zai iya haifarwa?”

ADVERTISEMENT

Ga dai bayanan nasu kamarhaka:

Sunana Princess Fatimah Mazadu Daga Jihar Gombe:

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

A gaskiya wannan matsalar takan faru ne a tsakanin ma’auratan da basa son juna sosai, hadin gida (auren dangi), ko babbar matsala na karya alkawari tsakaninsu, abu ne kuma wanda bai kamata ana yi wa yara hukuncin da ba laifinsu, wannan a bayyane cin zali ne da shirin maida yaro kangarerre. Ba shi da wani amfani sai illah, dan ya kan maida yaro ya zamo baya tausayin iyayenshi, kullum yana cikin jimamin rayuwarsa a duk sanda iyayensa suka samu sabani to, a kanshi ko a kansu za a huce haushi. Babbar matsala ma, dan zai sanya kokwanto a zuciyar yaransu na cewa iyayen nasu anya suna sonsu kuwa? Ko su kadai Allah ya bawa irin wadannan iyayen?, za su kasance suna turrr da halayen iyayen da irin rayuwar da Allah ya jarabcesu da shi. Shawara daya ce a duk sanda maaurata suka samu sabani kar su bari zuciyarsu ta ja su ga bakantawa yaransu dalilin nasu bakin cikin, su kiyaye sauke takaicinsu a kan yaransu dan watarana zuciya za ta kaisu ta bari cike da da-na-sani, dan basu san irin raunin da watarana za su yi wa yarannasu ba, gwargwadan bacin ransu gwargwadon illar da za su yi wa yaransu, Allah ya kare mu da wanann zuciyar ya kuma shirya mu ya shirya mana zuriya.

 

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Abin da hakan ke nufi hauka da rashin sanin yakamata. Ba shi da amfani sai rashin amfanin kansa domin na farko ta dauki alhakin yaransu, sannan kuma hakan sai dai ya kara tunzura maigidan. Babba ma kuwa domin idan uwa ta sake wannan ya zama al’adarta to ta sani watarana za ta iya rasa aurenta ko kuma ta rasa biyayya daga yaron da ake gallazawa da zarar ya gano abin da yake faruwa domin shi uban kansa zai iya dinga jawo yaron a jikinsa har sabon da yayi da mamansa ya koma kan uban. Shawarata a nan ita ce gaskiya su guji irin wannan halin da dabi’ar domin shi fa zagin iyaye ko muzgunawa yaro da iyaye suke yi baki suke wa yaro ba wai sai sun ce Allah yayi wadaran yaro ba kun ga kenan yaro tun yana karami mamansa ta jawo masa aibu tun yana karami bai ji ba bai gani ba don haka gaskiya mu iyaye muna sanin abin da za mu dinga furtawa yaranmu ko da ya ki ne ya faru tsakanin iyayensa din ba ma wani sabani ba. Allah ya kyauta ya shirya mana zurya amin.

 

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To hakika iyaye masu irin wannan dabi’a ko hali suna kuskure ne, kuma wannan kuskuren da suke zai bibiye su har karshen rayuwar su, domin dalilin wannan gallazawa da suke tana haddasa kiyayya a tsakaninsu da yaran ta har abada. Babu wani amfani domin shi fa yaro ba shi yayi laifi ba, kuma ita ma danta ne ba wai na uban ne shi kadai ba, don haka bai kamata ta musguna masa ba, saboda wai don ta rama abun da ubansa yayi mata sam-sam bai dace ba. Sosai ma kuwa, domin kuwa cigaban da yin hakan zai iya haifar da tsana a tsakanin ta da yaron kuma shi uban yaron za ta fita daga ransa wanda hakan ka’iya jawo mutuwar aure ko kuma rashin mutunta juna a zamantakewar aure. To ni dai shawara ta a nan ita ce ya kamata iyaye suna kokarin magance matsalar zaman takewar su ta aure a tsakaninsu ba tare da sa ‘ya’yansu a ciki ba, domin hakan zai taimaka wajen cigaba da zama tare da juna da samun hadin kai a tsakanin iyalai.

 

Sunana Hafsat Sa’eed Daga Jihar Neja:

Ni dai a nawa tunanin idan ka yi haka dan ka batawa maigidan rai ba abu ne me amfani ba kuma babu fa’ida a cikin hakan, tunda kuwa kai ka haifi danka da cikinka yadda ka ji ciwon haihuwarshi shi mijin bai ji ciwon ba, wani namijin ma babu ruwanshi dan kin gallazawa danki. Matsalar da hakan zai iya haifarwa shi ne; yaron zai ji tsanar uwar a ransa. Shawarata ya kamata duk abin da namiji zai yi miki to, ya tsaya tsakaninki da shi.

 

Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:

Hakika wannan tana faruwa a tsakanin ma’aurata kuma ana yin hakanne don munanawa daya barayin wanda hakan ba dai dai bane. Yin haka ba shi da wani amfani karshe ma matsala yake haifarwa a tsakanin ma’aurata ko kuma tsakanin yara da iyayensu. Tabbas hakan yana haifar da matsala domin yana kawo sabani tsakanin ma’aurata wanda har yana iya zama sanadin auren sannan kuma yana kawo kiyaiya tsakanin yara da iyayensu. Shawara a nan ita ce iyaye mata su ji tsoron Allah su daina aikata hakan domin laifin wani baya shafar wani.

 

Sunana Idris Haruna Zareku Miga A Jihar Jigawa:

A kan wannan batun, ana iya cewa iyaye da suke gallazawa ‘ya’yensu suna gudanar da abin kunya da rashin tausayi, wannan na iya haifar da matsaloli masu yawa ga ci gaban yara, tun daga damuwa da rashin jin dadin jiki har zuwa rashin yarda da kai. Abubuwan da zai iya zama amfaninsa za a iya ganin gallazawa a matsayin hanyar koyar da ‘ya’yansu darussa na tarbiyya da zama masu biyayya da jimrewa a cikin al’umma. Gallazawa na iya haifar da damuwa da rashin jin dadi ga ‘ya’yan, wanda zai iya shafar ingancin huldar su da iyayensu. Sannan hakan na iya haifar da rashin yarda tsakanin ‘ya’ya da iyayensu, wanda zai iya janyo rashin zaman lafiya a cikin iyali. Shawarwari ga iyaye mata da su yawaita tattaunawa tare da ‘ya’yansu, su saurari ra’ayoyinsu da jin damuwarsu, su yi kokarin gina amincewa da ‘ya’yansu ta hanyar kyakkyawar gwaninta da goyon baya, maimakon matsin lamba. Su fahimci cewa bai dace ba su rika hargitsa ‘yanu’wansu domin abubuwan da ba su ji dadin su ba, sai dai kyautata hanyar da za su koyar da su kyawawan dabi’u.

Mata
Rabi'at Sidi Bala
+ posts Bio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Mata
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Taskira

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
Taskira

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
Taskira

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Next Post
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

Ya Kamata Mata 'Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.