• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zan Samar Da Sabuwar Nijeriya – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Dakta Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da kwamitin yakin neman zabensa, wanda shi da kansa yake jagoranta.

Kwamitin mai mambobi 1,053 a Abuja, wanda Kwankwaso ya tabbatar da cewa samar da sabuwar Nijeriya abu ne mai yiwuwa a karkashin shugabancinsa.

  • 2023: Irin Alkawuran Da Kwankwaso Ya Yi Wa ‘Yan Jihar Delta

“Yawan mutane masu daraja da mutunci da suka taru a wannan babban dakin taro da nufin a hadu a yi tafiyar mai matukar muhimmanci. Dalilin da ya sanya aka gudanar da taron a haka shi ne don a sami natsuwa tare da la’akari da yanayin tsaro a Nijeriya a halin da ake ciki ta yadda ba za a sanya mutane cikin hatsari ba, sakamakon tsaro don dai kawai halarci taron kaddamar da dan takara,” kamar yadda ya fada.

Ya kara da cewa kwamitin yakin neman zaben na shugaban kasa tare da miliyoyin ‘yan sa-kai da magoya baya da suke dukkanin jihohin Nijeriya 36 har da Babban Birnin Tarayya Abuja za su ci gaba da aiki kafada da kafada domin tabbatar da nasarar jam’iyyar NNPP a babban zabe.

A cewarsa, samun sabuwar Nijeriya a karkashinsa na nufin, “Nijeriyar da za tabbatar da adalci da tsoron Allah, Nijeriya da za a tabbatar da samun ingantaccen tsaro, Nijeriyar da za a tabbatar da zaman lafiya da lumana, Nijeriyar da za a tabbatar da daidaito ga kowanne dan kasa, Nijeriyar da za a sami ingantaccen ilimi da kula da bangaren lafiya ta hanyar samar da kayayyakin aiki na zamani ga kowa, Nijeriyar da za a rika gudanar da shugabanci na adalci da tausasawa ga kowa.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

“Wannan shi ne sabuwar Nijeriya da mu a jam’iyyar NNPP muke aiki ba dare ba rana da za a fara daga ranar 29 ga watan Mayun 2023 da izinin Allah.”

Kwankwaso ya ce zai fara gudanar da yakin neman zabensa a yanki Bauchi a ranar 12 ga watan Janairu na Arewa maso Gabas. A cewarsa, kwamitin yakin neman zaben da ke sadaukarwa da gaskiya da rikon amana da aiki tukuru ga su da kwarewa da tsoron Allah da zai amfanar da ‘yan Nijeriya wanda za su tabbatar da samun nasarar Rabiu Musa Kwankwaso a zaben 2023.

A hannu guda kuwa, mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Buishop Isaac Idahosa ya kaddamar da sashin bayar da tallafin kudi don yakin neman zabe mai adireshin donation.rmkidahosa.com.
Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su bayar da tallafi na yakin neman zabe. Ya ce a duk lokacin da kake son abu, dole ka zuba jari a cikinsa.”

Haka kuma ya ce, kwamitrin yakin neman zaben shugaban kasa ba zai yi siyasar kudi ba ne, amma yana bukatar kudi na tafiye-tafiye. Ya tabbatar da cewa za a rantsare da shi mataimakin shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace DPO A Jihar Filato

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

2 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Babu Barazanar Kai Hari A Kano – ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace DPO A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.