ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zan Samar Da Sabuwar Nijeriya – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Dakta Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da kwamitin yakin neman zabensa, wanda shi da kansa yake jagoranta.

Kwamitin mai mambobi 1,053 a Abuja, wanda Kwankwaso ya tabbatar da cewa samar da sabuwar Nijeriya abu ne mai yiwuwa a karkashin shugabancinsa.

  • 2023: Irin Alkawuran Da Kwankwaso Ya Yi Wa ‘Yan Jihar Delta

“Yawan mutane masu daraja da mutunci da suka taru a wannan babban dakin taro da nufin a hadu a yi tafiyar mai matukar muhimmanci. Dalilin da ya sanya aka gudanar da taron a haka shi ne don a sami natsuwa tare da la’akari da yanayin tsaro a Nijeriya a halin da ake ciki ta yadda ba za a sanya mutane cikin hatsari ba, sakamakon tsaro don dai kawai halarci taron kaddamar da dan takara,” kamar yadda ya fada.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa kwamitin yakin neman zaben na shugaban kasa tare da miliyoyin ‘yan sa-kai da magoya baya da suke dukkanin jihohin Nijeriya 36 har da Babban Birnin Tarayya Abuja za su ci gaba da aiki kafada da kafada domin tabbatar da nasarar jam’iyyar NNPP a babban zabe.

A cewarsa, samun sabuwar Nijeriya a karkashinsa na nufin, “Nijeriyar da za tabbatar da adalci da tsoron Allah, Nijeriya da za a tabbatar da samun ingantaccen tsaro, Nijeriyar da za a tabbatar da zaman lafiya da lumana, Nijeriyar da za a tabbatar da daidaito ga kowanne dan kasa, Nijeriyar da za a sami ingantaccen ilimi da kula da bangaren lafiya ta hanyar samar da kayayyakin aiki na zamani ga kowa, Nijeriyar da za a rika gudanar da shugabanci na adalci da tausasawa ga kowa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Wannan shi ne sabuwar Nijeriya da mu a jam’iyyar NNPP muke aiki ba dare ba rana da za a fara daga ranar 29 ga watan Mayun 2023 da izinin Allah.”

Kwankwaso ya ce zai fara gudanar da yakin neman zabensa a yanki Bauchi a ranar 12 ga watan Janairu na Arewa maso Gabas. A cewarsa, kwamitin yakin neman zaben da ke sadaukarwa da gaskiya da rikon amana da aiki tukuru ga su da kwarewa da tsoron Allah da zai amfanar da ‘yan Nijeriya wanda za su tabbatar da samun nasarar Rabiu Musa Kwankwaso a zaben 2023.

A hannu guda kuwa, mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Buishop Isaac Idahosa ya kaddamar da sashin bayar da tallafin kudi don yakin neman zabe mai adireshin donation.rmkidahosa.com.
Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su bayar da tallafi na yakin neman zabe. Ya ce a duk lokacin da kake son abu, dole ka zuba jari a cikinsa.”

Haka kuma ya ce, kwamitrin yakin neman zaben shugaban kasa ba zai yi siyasar kudi ba ne, amma yana bukatar kudi na tafiye-tafiye. Ya tabbatar da cewa za a rantsare da shi mataimakin shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Babu Barazanar Kai Hari A Kano – ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace DPO A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.