ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zan Samar Da Sabuwar Nijeriya – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Dakta Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da kwamitin yakin neman zabensa, wanda shi da kansa yake jagoranta.

Kwamitin mai mambobi 1,053 a Abuja, wanda Kwankwaso ya tabbatar da cewa samar da sabuwar Nijeriya abu ne mai yiwuwa a karkashin shugabancinsa.

  • 2023: Irin Alkawuran Da Kwankwaso Ya Yi Wa ‘Yan Jihar Delta

“Yawan mutane masu daraja da mutunci da suka taru a wannan babban dakin taro da nufin a hadu a yi tafiyar mai matukar muhimmanci. Dalilin da ya sanya aka gudanar da taron a haka shi ne don a sami natsuwa tare da la’akari da yanayin tsaro a Nijeriya a halin da ake ciki ta yadda ba za a sanya mutane cikin hatsari ba, sakamakon tsaro don dai kawai halarci taron kaddamar da dan takara,” kamar yadda ya fada.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa kwamitin yakin neman zaben na shugaban kasa tare da miliyoyin ‘yan sa-kai da magoya baya da suke dukkanin jihohin Nijeriya 36 har da Babban Birnin Tarayya Abuja za su ci gaba da aiki kafada da kafada domin tabbatar da nasarar jam’iyyar NNPP a babban zabe.

A cewarsa, samun sabuwar Nijeriya a karkashinsa na nufin, “Nijeriyar da za tabbatar da adalci da tsoron Allah, Nijeriya da za a tabbatar da samun ingantaccen tsaro, Nijeriyar da za a tabbatar da zaman lafiya da lumana, Nijeriyar da za a tabbatar da daidaito ga kowanne dan kasa, Nijeriyar da za a sami ingantaccen ilimi da kula da bangaren lafiya ta hanyar samar da kayayyakin aiki na zamani ga kowa, Nijeriyar da za a rika gudanar da shugabanci na adalci da tausasawa ga kowa.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Wannan shi ne sabuwar Nijeriya da mu a jam’iyyar NNPP muke aiki ba dare ba rana da za a fara daga ranar 29 ga watan Mayun 2023 da izinin Allah.”

Kwankwaso ya ce zai fara gudanar da yakin neman zabensa a yanki Bauchi a ranar 12 ga watan Janairu na Arewa maso Gabas. A cewarsa, kwamitin yakin neman zaben da ke sadaukarwa da gaskiya da rikon amana da aiki tukuru ga su da kwarewa da tsoron Allah da zai amfanar da ‘yan Nijeriya wanda za su tabbatar da samun nasarar Rabiu Musa Kwankwaso a zaben 2023.

A hannu guda kuwa, mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Buishop Isaac Idahosa ya kaddamar da sashin bayar da tallafin kudi don yakin neman zabe mai adireshin donation.rmkidahosa.com.
Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su bayar da tallafi na yakin neman zabe. Ya ce a duk lokacin da kake son abu, dole ka zuba jari a cikinsa.”

Haka kuma ya ce, kwamitrin yakin neman zaben shugaban kasa ba zai yi siyasar kudi ba ne, amma yana bukatar kudi na tafiye-tafiye. Ya tabbatar da cewa za a rantsare da shi mataimakin shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Babu Barazanar Kai Hari A Kano – ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace DPO A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Kwankwaso

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kwankwaso

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.