ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zan Samar Da Sabuwar Nijeriya – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Dakta Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da kwamitin yakin neman zabensa, wanda shi da kansa yake jagoranta.

Kwamitin mai mambobi 1,053 a Abuja, wanda Kwankwaso ya tabbatar da cewa samar da sabuwar Nijeriya abu ne mai yiwuwa a karkashin shugabancinsa.

  • 2023: Irin Alkawuran Da Kwankwaso Ya Yi Wa ‘Yan Jihar Delta

“Yawan mutane masu daraja da mutunci da suka taru a wannan babban dakin taro da nufin a hadu a yi tafiyar mai matukar muhimmanci. Dalilin da ya sanya aka gudanar da taron a haka shi ne don a sami natsuwa tare da la’akari da yanayin tsaro a Nijeriya a halin da ake ciki ta yadda ba za a sanya mutane cikin hatsari ba, sakamakon tsaro don dai kawai halarci taron kaddamar da dan takara,” kamar yadda ya fada.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa kwamitin yakin neman zaben na shugaban kasa tare da miliyoyin ‘yan sa-kai da magoya baya da suke dukkanin jihohin Nijeriya 36 har da Babban Birnin Tarayya Abuja za su ci gaba da aiki kafada da kafada domin tabbatar da nasarar jam’iyyar NNPP a babban zabe.

A cewarsa, samun sabuwar Nijeriya a karkashinsa na nufin, “Nijeriyar da za tabbatar da adalci da tsoron Allah, Nijeriya da za a tabbatar da samun ingantaccen tsaro, Nijeriyar da za a tabbatar da zaman lafiya da lumana, Nijeriyar da za a tabbatar da daidaito ga kowanne dan kasa, Nijeriyar da za a sami ingantaccen ilimi da kula da bangaren lafiya ta hanyar samar da kayayyakin aiki na zamani ga kowa, Nijeriyar da za a rika gudanar da shugabanci na adalci da tausasawa ga kowa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Wannan shi ne sabuwar Nijeriya da mu a jam’iyyar NNPP muke aiki ba dare ba rana da za a fara daga ranar 29 ga watan Mayun 2023 da izinin Allah.”

Kwankwaso ya ce zai fara gudanar da yakin neman zabensa a yanki Bauchi a ranar 12 ga watan Janairu na Arewa maso Gabas. A cewarsa, kwamitin yakin neman zaben da ke sadaukarwa da gaskiya da rikon amana da aiki tukuru ga su da kwarewa da tsoron Allah da zai amfanar da ‘yan Nijeriya wanda za su tabbatar da samun nasarar Rabiu Musa Kwankwaso a zaben 2023.

A hannu guda kuwa, mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Buishop Isaac Idahosa ya kaddamar da sashin bayar da tallafin kudi don yakin neman zabe mai adireshin donation.rmkidahosa.com.
Ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su bayar da tallafi na yakin neman zabe. Ya ce a duk lokacin da kake son abu, dole ka zuba jari a cikinsa.”

Haka kuma ya ce, kwamitrin yakin neman zaben shugaban kasa ba zai yi siyasar kudi ba ne, amma yana bukatar kudi na tafiye-tafiye. Ya tabbatar da cewa za a rantsare da shi mataimakin shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Babu Barazanar Kai Hari A Kano – ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace DPO A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.