• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gun taron ministoci game da tantance ayyukan aiwatar da sakamakon da aka samu a dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da ya gudana a birnin Changsha na Sin a kwanan nan, kasar Sin ta sanar da cewa, za ta yafe harajin fito kan dukkan kayayyakin kasashe 53 dake nahiyar Afirka da ta kulla huldar diplomasiyya da su. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin tana kokarin cika alkawarin da ta yi na gina “al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya”.

Ban da kasashe 33 masu karancin tattalin arziki dake nahiyar Afirka, da tuni suka ci gajiyar manufar Sin ta yafe harajin kwastam, sabbin kasashe 20 dake Afirka da za su ci gajiyar manufar, sun hada da Najeriya, da Masar, da Afirka ta Kudu, da kuma Aljeriya, wato kasashe hudu mafi karfin tattalin arziki a Afirka. Wadannan kasashe, a bisa tushen karfinsu a fannin tattalin arziki, za su iya amfani da manufar kasar Sin wajen kara habaka bangaren fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin Sin sosai. Bugu da kari, game da wasu kasashen Afirka da ke da gibin ciniki da kasar Sin, manufar yafe haraji ta kasar za ta taimaka wajen daidaita cinikayyarsu da kasar Sin.

  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

Idan aka waiwayi yadda aka raya dangantakar tattalin arziki da ciniki tsakanin Sin da Afirka cikin shekaru 20 da suka gabata, za mu iya ganin cewa, manufar rangwame a fannin harajin kwastam da kasar Sin ta samar wa kasashen Afirka ta yi ta fadada zuwa fannoni daban daban.

Tun a shekarar 2005, kasar Sin ta fara daukar matakan rage harajin fito kan kayayyakin kasashen Afirka da ke da raunin tattalin arziki, kuma ya zuwa shekarar 2010, manufar ta shafi kashi 60 cikin 100 na kayayyakin kasashe 26 dake nahiyar Afirka. Sa’an nan, daga shekarar 2022, kasar Sin sannu a hankali ta fara aiwatar da matakin yafe haraji kan kaso 98% na kayayyakin kasashe 27 dake Afirka. Bayan haka, a gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2024 da aka gudanar a birnin Beijing, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya sanar da yafe harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da ake shigowa kasar Sin daga kasashen Afirka 33 da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki wadanda suka kulla huldar diplomasiyya tare da ita. Sai kuma ga shi a yanzu, manufar yafe haraji ta kasar Sin ta shafi dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diplomasiyya tare da ita.

Ba kamar wasu matakan ciniki da suka jibanci Afirka, da kasashen yamma suka gabatar a baya ba, wadanda ke shafar manufofin siyasa da yunkurin gyaran tsare-tsaren Afirka, manufofin kasar Sin suna da halayen musamman guda uku: Wato da farko, ba a taba gindaya sharadi na siyasa ba. Kana na biyu, manufofin suna dorewa. Gami da na uku, wato kasar na tare da burin tabbatar da ci gaban tattalin arzikin Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Ta hanyar inganta manufar yafe harajin kwastam a kai a kai, kasar Sin ta samar da yanayin kasuwanci mai karko a kasashen Afirka. Bugu da kari, kasar Sin tana kallon manufofinta na rangwame a matsayin matakan tabbatar da burin samun ci gaba, inda take kokarin kyautata tsarin cinikayyar waje na kasashen Afirka, da kuma ba da goyon baya wajen raya masana’antu, da habaka tsare-tsaren tattalin arziki a Afirka.

Dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tabbatar da ci gabanta da kasashen Afirka na bai daya, shi ne domin ra’ayinta game da dangantakar dake tsakaninta da Afirka, wato al’ummar Sin da Afirka suna da makomar bai daya a nan gaba. A ganin kasar Sin, ita da Afirka suna da tarihi masu kama da juna, da kuma bukatun bai daya na raya kasa. Sa’an nan, a zamanin da muke ciki, yayin da ake fuskantar sauye-sauye a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, kasashe masu tasowa na cikin wani yanayi mai wuya ta fuskar raya tattalin arzikinsu. Saboda haka, Sin da Afirka ba za su iya cimma burinsu na samun ci gaban bai daya ba, sai dai ta hanyar hadin gwiwa da juna, a bangarorin tabbatar da adalci da gaskiya a duniya , da bude kofa, da tabbatar da moriyar kowa, da kyautata muhalli, da kuma kiyaye zaman lafiya. Bisa kokarin da ake na sauya nagartaccen tunani zuwa hakikanan matakai, ko shakka babu za mu shaida karin nasarorin da Sin da Afirka za su samu, a kokarinsu na zamanantar da al’ummunsu tare. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

Next Post

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Related

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

1 day ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

4 days ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

1 week ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

1 week ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

2 weeks ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

2 weeks ago
Next Post
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

June 18, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

June 18, 2025
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

June 18, 2025
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

June 18, 2025
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

June 18, 2025
Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.