• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aiki: An Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC/TUC, Za A Koma Teburin Sulhu

by Muhammad
12 months ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyoyin Kwadago da Gwamnatin Tarayya sun cimma matsaya kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa tare da kudurin ci gaba da gudanar da harkokin yau da kullum na tsawon mako guda don sake bai wa kwamitin mafi karancin albashi na kasa dama har a samu a cimma matsaya ta karshe.

Bayanin hakan ya fito da yammacin ranar Litinin a karshen taron da kungiyoyin Kwadago na NLC/TUC su ka gudunar da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, a sakamakon bukatar da ake da ita na samun damar ci gaba da tattaunawa da kwamitin da ke kula da mafi karancin albashi na kasa kan sabon mafi karancin albashi.

  • Da Ɗuminsa: An Rufe Ƙofa Tsakanin Ƙungiyar Ƙwadago Da Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Yajin Aiki: Ƙungiyar Ƙwadago Ta Rufe Filayen Jirgin Saman Legas Da Abuja

LEADERSHIP HAUSA ta ruwaito cewa a ranar Litinin mambobin kungiyar kwadago ta kasa NLC da TUC suka shiga yajin aikin gama-gari a kasa baki daya, domin neman amsa bukatar su ta neman karin mafi karancin albashin ma’aikata da kuma sauya farashin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan. wanda ya gurgunta ayyukan gwamnati da masana’antu masu zaman kansu a fadin Nijeriya.

A wata sanarwa da aka fitar a karshen taron da aka gudanar da ministan yada labarai da takwaransa na kwadago da samar da ayyuka, Mohammed Idris da Nkiruka Onyejeocha, daga bangaren gwamnatin tarayya, da shugabannin NLC da TUC, Joe Ajaero da Festus Osifo suka amince da shi.

A taron an amince da wasu kudurori guda hudu a matsayin hanyar kawo karshen takaddama kan karin albashin.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

“Shugaban kasa, ya kuduri aniyar biyan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa da ya haura N60,000;

“Saboda abubuwan da suka gabata, kwamitin zai ci gaba da gana wa a cikin mako a kullun har zuwa lokacin da za a cimma matsaya ta karshe kan mafi karancin albashi na kasa;

“Babu wani ma’aikaci da za a ci zarafinsa a sakamakon shiga yajin aikin,” Cewar yarjejeniyar gwamnati da kungiyoyin kwadago.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiMafi Karancin AlbashiNlcTUCYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

Next Post

Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi 

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

17 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

23 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 day ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

1 day ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

1 day ago
Next Post
Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi 

Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi 

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.