ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aiki: An Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC/TUC, Za A Koma Teburin Sulhu

by Muhammad
2 years ago
Yajin Aiki

Kungiyoyin Kwadago da Gwamnatin Tarayya sun cimma matsaya kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa tare da kudurin ci gaba da gudanar da harkokin yau da kullum na tsawon mako guda don sake bai wa kwamitin mafi karancin albashi na kasa dama har a samu a cimma matsaya ta karshe.

Bayanin hakan ya fito da yammacin ranar Litinin a karshen taron da kungiyoyin Kwadago na NLC/TUC su ka gudunar da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, a sakamakon bukatar da ake da ita na samun damar ci gaba da tattaunawa da kwamitin da ke kula da mafi karancin albashi na kasa kan sabon mafi karancin albashi.

  • Da Ɗuminsa: An Rufe Ƙofa Tsakanin Ƙungiyar Ƙwadago Da Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Yajin Aiki: Ƙungiyar Ƙwadago Ta Rufe Filayen Jirgin Saman Legas Da Abuja

LEADERSHIP HAUSA ta ruwaito cewa a ranar Litinin mambobin kungiyar kwadago ta kasa NLC da TUC suka shiga yajin aikin gama-gari a kasa baki daya, domin neman amsa bukatar su ta neman karin mafi karancin albashin ma’aikata da kuma sauya farashin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan. wanda ya gurgunta ayyukan gwamnati da masana’antu masu zaman kansu a fadin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwa da aka fitar a karshen taron da aka gudanar da ministan yada labarai da takwaransa na kwadago da samar da ayyuka, Mohammed Idris da Nkiruka Onyejeocha, daga bangaren gwamnatin tarayya, da shugabannin NLC da TUC, Joe Ajaero da Festus Osifo suka amince da shi.

A taron an amince da wasu kudurori guda hudu a matsayin hanyar kawo karshen takaddama kan karin albashin.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Shugaban kasa, ya kuduri aniyar biyan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa da ya haura N60,000;

“Saboda abubuwan da suka gabata, kwamitin zai ci gaba da gana wa a cikin mako a kullun har zuwa lokacin da za a cimma matsaya ta karshe kan mafi karancin albashi na kasa;

“Babu wani ma’aikaci da za a ci zarafinsa a sakamakon shiga yajin aikin,” Cewar yarjejeniyar gwamnati da kungiyoyin kwadago.

Yajin Aiki
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi 

Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.