• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Dalibai Sun Yi Barazanar Rufe Tituna, Tashoshin Jirgin Sama Da Na Kasa

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Yajin Aikin ASUU: Dalibai Sun Yi Barazanar Rufe Tituna, Tashoshin Jirgin Sama Da Na Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Reshen Dalibai na Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula na Arewa, da ke Jihar Kano (CNG-SW), sun yi barazanar rufe filayen jirgin sama da tashoshin jirgin kasa da kuma manyan titunan Arewa in har gwamnatin tarayya da ASUU ba su kawo karshen takaddamar yajin aikin da ke tsakaninsu ba.

Daliban sun yi barazanar rufe ofisoshin jam’iyyun siyasa a jihohi 19 da ke Arewacin Nijeriya.

  • Bayan Ruwan Wuta: Masu Garkuwa Sun kama Basarake A Jos
  • Hajjin Bana: Saudiya Ta Hana Amfani Da Gas Din Girki A Lokacin Aikin Hajji

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwa da ko’odinetan kungiyar Ambasada Khaleefa Nura Babujee, ya fitar ga manema labarai a Kano.

Ko’odinetan kungiyar, Babujee, Ya ce CNG-SW ta shiga damuwa kan yadda yajin aikin ASUU yaki ci yaki cinyewa.

A cewar ungiyar yajin aikin ya jefa ‘ya’yan talakawa cikin mawuyacin hali.

Labarai Masu Nasaba

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Ya kara da cewa tuni kungiyar ta yi shirin  daukar gabaran rubuta korafi ga sarakunan gargajiya, malaman addini, jami’an gwamnati da jami’an tsaro a kan su saka baki a kawo karshen yakin aikin.

“Idan haka ba ta samu ba, to za mu rufe filayen jirgin sama da tashoshin jirgin kasa tare damanyan titunan Arewacin Nijeriya.

“Za kuma mu rufe ofisoshin jam’iyyun siyasa a jihohi 19 na yankin Arewa,” in ji CNG-SW

Ya zuwa yanzu ASUU da gwamnatin tarayya sun gaza cimma matsaya don kawo karshen yajin aikin da suka jima suna yi.

A baya-bayan nan ma sai da dalibai a wasu jihohin Nijeriya da suka hada da Kano, Legas, Kaduna, Anambra da sauransu suka gudanar da zanga-zangar adawa da yajin aikin na ASUU.

Har ila yau, masu ruwa da tsaki a fannin ilimi sun sha kira ga bangarorin biyu da su yi kokarin samun fahimta don dalibai su koma bakin karatunsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUBarazanaDalibaiJami'o'iKaratuTakaddamaYajin AikiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Ruwan Wuta: Masu Garkuwa Sun kama Basarake A Jos

Next Post

Rabi Shehu Sharada: ‘Yan Siyasa Sun Ci Moriyar Ganga, Sun Yada Kwaurenta!

Related

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

37 minutes ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

5 hours ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

6 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

6 hours ago
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Labarai

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

8 hours ago
Next Post
Rabi Shehu Sharada: ‘Yan Siyasa Sun Ci Moriyar Ganga, Sun Yada Kwaurenta!

Rabi Shehu Sharada: ‘Yan Siyasa Sun Ci Moriyar Ganga, Sun Yada Kwaurenta!

LABARAI MASU NASABA

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

September 7, 2025
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

September 7, 2025
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

September 7, 2025
Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.