• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan AS’HABUL KAHFI Za Su Daukaka Kara Kan Hukuncin Kisa Ga Abduljabbar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Abduljabbar

Kungiyar As’habul Kahfu Warraqeen reshen jihar Bauchi ta sha alwashin daukaka kara dangane da hukuncin kisa da wata kotun shari’a ta yanke wa Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara a kwanakin baya.

 

A wani taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a ranar Litinin ta yi watsi da hukuncin da alkali Ibrahim Sarki Yola ya yanke tare da misalta hukuncin a matsayin wanda ke cike da kura-kurai da kuma son zuciya a ciki.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Sheikh Abduljabbar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Da ya ke karanta matsayarsu ga ‘yan jarida a shalkwatar ‘yan jarida da ke Bauchi (NUJ), Abdullahi Musa, Kakakin kungiyar, ya ce, da gangan Alkalin ya sauya batutuwan da suke akwai domin kaiwa ga matakin yanke hukuncin kisa ga malamin nasu.

 

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Kungiyar ta zargi gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje da kitsa komai domin cimma manufarsa na dakile aniyar Abduljabbar Kabara bisa sukarsa da yake yi kan rashawa da cin hanci.

 

Musa ya ce, “Mun cimma matsar daukaka kara ne zuwa kotun sama domin neman hakki ta hanyar shari’a, domin kwata-kwata ba mu amince da hukuncin Ibrahim Sarki Yola ba; kuma abubuwan da aka yi wa malaminmu ya saba wa dokokin kare hakkin jama’a musamman dokar ‘yancin yin addini yadda mutum ya fahimta kamar yadda ke kunshe cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

 

“Muna sane da wasu Malamai da suke adawa da Abduljabbar wadanda suka aikata laifuka na batanci da dama a wa’azozi da jawabansu amma babu wani abun da aka musu suna kan cigaba da wa’azozinsu ba tare da musgunawa ba.”

 

Kungiyar ta jero wasu da ta zarga da cewa su ma sun taba yin batanci da suka hada da Qaribu Kabara, Abdulrazak Yahya Haifan, Abbas Jega, Jalo Jalingo, Ahmad Gumi, Abdulwahab Abdullah da Sani Rijiyar Lemo amma babu wani da ya tuhumesu “Saboda su na kusa ko tare da masu mulki, su na nan a cikin ‘yancinsu a yayin da mu kuma shugabanmu wanda babu laifin da ya yi yana kan fuskantar shari’a.”

 

A cewarsu, zargin batanci da ake yi wa Abduljabbar Nasiru Kabara babu komai a ciki illa salon yakarsa da kokarin kawo karshensa hadi da bata masa suna ta kowace hanya da wasu wadanda ba su jin dadin wa’azinsa ciki har da gwamna Ganduje suka yi, “Duk wadannan abubuwan tsararru ne. Haka suka tsara domin cimma manufofinsu da ke boye.”

 

“Tun da farko mu ba mu amince da hukuncin ba, saboda mun yi imanin cewa gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje da wasu Malamai a jihar da aka sani na tsawon lokaci suke yakar Abduljabbar ne suka kitsa hakan ta hanyar masa karya da qage gami da jingina masa laifin batanci wanda kai tsaye sharri ne. Su kuma suka juya shaidu har aka kawo wannan matakin,” kungiyar ta yi zargi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
Manyan Labarai

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Next Post
Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.