• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan AS’HABUL KAHFI Za Su Daukaka Kara Kan Hukuncin Kisa Ga Abduljabbar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Batanci Kan Manzon Allah: Kotu Ta Ci Tarar Sheikh Abduljabbar Naira Miliyan 10
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar As’habul Kahfu Warraqeen reshen jihar Bauchi ta sha alwashin daukaka kara dangane da hukuncin kisa da wata kotun shari’a ta yanke wa Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara a kwanakin baya.

 

A wani taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a ranar Litinin ta yi watsi da hukuncin da alkali Ibrahim Sarki Yola ya yanke tare da misalta hukuncin a matsayin wanda ke cike da kura-kurai da kuma son zuciya a ciki.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Sheikh Abduljabbar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Da ya ke karanta matsayarsu ga ‘yan jarida a shalkwatar ‘yan jarida da ke Bauchi (NUJ), Abdullahi Musa, Kakakin kungiyar, ya ce, da gangan Alkalin ya sauya batutuwan da suke akwai domin kaiwa ga matakin yanke hukuncin kisa ga malamin nasu.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Kungiyar ta zargi gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje da kitsa komai domin cimma manufarsa na dakile aniyar Abduljabbar Kabara bisa sukarsa da yake yi kan rashawa da cin hanci.

 

Musa ya ce, “Mun cimma matsar daukaka kara ne zuwa kotun sama domin neman hakki ta hanyar shari’a, domin kwata-kwata ba mu amince da hukuncin Ibrahim Sarki Yola ba; kuma abubuwan da aka yi wa malaminmu ya saba wa dokokin kare hakkin jama’a musamman dokar ‘yancin yin addini yadda mutum ya fahimta kamar yadda ke kunshe cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

 

“Muna sane da wasu Malamai da suke adawa da Abduljabbar wadanda suka aikata laifuka na batanci da dama a wa’azozi da jawabansu amma babu wani abun da aka musu suna kan cigaba da wa’azozinsu ba tare da musgunawa ba.”

 

Kungiyar ta jero wasu da ta zarga da cewa su ma sun taba yin batanci da suka hada da Qaribu Kabara, Abdulrazak Yahya Haifan, Abbas Jega, Jalo Jalingo, Ahmad Gumi, Abdulwahab Abdullah da Sani Rijiyar Lemo amma babu wani da ya tuhumesu “Saboda su na kusa ko tare da masu mulki, su na nan a cikin ‘yancinsu a yayin da mu kuma shugabanmu wanda babu laifin da ya yi yana kan fuskantar shari’a.”

 

A cewarsu, zargin batanci da ake yi wa Abduljabbar Nasiru Kabara babu komai a ciki illa salon yakarsa da kokarin kawo karshensa hadi da bata masa suna ta kowace hanya da wasu wadanda ba su jin dadin wa’azinsa ciki har da gwamna Ganduje suka yi, “Duk wadannan abubuwan tsararru ne. Haka suka tsara domin cimma manufofinsu da ke boye.”

 

“Tun da farko mu ba mu amince da hukuncin ba, saboda mun yi imanin cewa gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje da wasu Malamai a jihar da aka sani na tsawon lokaci suke yakar Abduljabbar ne suka kitsa hakan ta hanyar masa karya da qage gami da jingina masa laifin batanci wanda kai tsaye sharri ne. Su kuma suka juya shaidu har aka kawo wannan matakin,” kungiyar ta yi zargi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Bikin Fina-Finai Na Tsibirin Hainan Karo Na 4 

Next Post

Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

3 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

4 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

5 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

6 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

10 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

11 hours ago
Next Post
Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

LABARAI MASU NASABA

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.