• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: Sama Da Mutum Miliyan Daya Suka Yi Gudun Hijira A Arewa Maso Yamma – IOM

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
‘Yan Bindiga: Sama Da Mutum Miliyan Daya Suka Yi Gudun Hijira A Arewa Maso Yamma – IOM
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutum 1,087,875 ne suka rasa matsugunansu sakamakon yawaitar ayyukan ‘yan bindiga da masu satar shanu da kuma masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya.

Rikicin ya fi shafar mata da yara, kashi 54 mata da kashi 56 na yara sun yi gudun hijira a Jihar Katsina, kuma jimillar mutanen da lamarin ya shafa sun kai 223,473.

  • Bayanin Da Amurka Ta Yi Kan Kudurin MDD Yaudara Ce Da Ta YI Wa Al’umma

An bayyana hakan ne a taron kaddamar da shirin sasanta rikici da sulhu a yankin arewa maso yammacin Nijeriya a hukumance, wanda hukumar kula da shige da fice ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM) ta shirya a Babban Birnin Jihar Katsina a ranar Litinin.

Shugaban hukumar ta IOM, Laurent De Boeck, ya bayyana cewa arewa maso yamma na fama da rikice-rikice tun daga shekarar 2014, wanda ya kai ga gudanar da bincike a watan Oktoban 2022 don gano karuwar tashe-tashen hankula, wanda ya shafi kimanin mutum sama da miliyan daya, a cikin wannan adadi kashi 29 cikin 100 ‘yan asalin Jihar Katsina ne.

Ya kuma kara tabbatar da cewa IOM, cibiyar habaka dimokuradiyya tare da taimakon Kungiyar Tarayyar Turai sun hada kai da gwamnatin Jihar Katsina domin inganta tsarin shiri sulhunta al’umma a jihar, da nufin rage rikice-rikice da inganta shirin samar da zaman lafiya a cikin gida da rage radadin talauci da inganta albarkatun kasa na arewa maso yammacin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Aikin wanda ya kai kimanin watanni 18, ya fara ne tun daga Janairu 2022 zuwa Yuli 2023, za a gudanar da shi a kananan hukumomi hudu da suka hada da Dandume, Danmusa, Batsari da Jibia a Jihar Katsina.

Shima da yake jawabi a madadin gwamnatin jihar, kwamishinan harkokin cikin gida da tsaro, Nasiru Muazu Danmusa, ya gode wa abokan hulda na kasa da kasa kan wannan gagarimin aikin. Ya ce jihar na bukatar karin tallafi domin yaki da rashin tsaro da ya addabi wasu sassan jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarayyar Turai Ta Ci Tarar Facebook Dala Biliyan 1.3

Next Post

Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

Related

IOM
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
IOM

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.