ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
10 months ago
'Yan Bindiga

Maganar sulhu da bbarayin daji a Jihar Katsina y afara haifar da da mai ido, abin da Bahaushe ke cewa abu kamar wasa karamar magana ta zama babba.

A bayan dai gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ta ce matsayarta kan batun sunlhu da ‘yan bindiga sun yi hannun riga.

To sai dai, wannan batu fa a Katsina yanzu ba haka yake ba, domin kuwa al’ummomin da suka yanke shawarar yin sulhu da ‘yan ta’adda domin su zauna lafiya, suna cin amfanin hakan.

ADVERTISEMENT

A yayin da matsayar gwamnati ke cin karo da wannan sulhu, an sha ruwaito cewa Gwamnan Radda yana cewa babu wata hanya da yake ganin zai iya yin sulhu da dan ta’adda, sai dai dan ta’adda ne ya ji wuta daga jami’an tsaro ya mika kansa kuma ya yarda a zauna lafiya.

Zuwa yanzu dai kananan hukumomi guda bakwai ne suka shiga sulhu da barayin daji domin neman tsira da ransu da kuma ci gaba da yin hidimominsu na yau da kullum.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Karamar karamar hukumar Jibiya ita ce ta fara shirya taro domin yin sulhu da ‘yan bindigar, sai dai kuma ba a ga wakilin gwamnatin Jihar Katsina a wannan sulhu ba, amma dai an ga shugaban karamar hukumar da sauran jami’an tsaro da ake zargin daga Abuja suke halartar irin wannan taro.

An yi wannan sulhu a karamar hukumar Jibiya kimanin wata hudu da suka gabata, kuma al’amurra na ci gaba da tafiya yadda ake so, zuwa yanzu dai al’ummomi a wannan karamar hukumar na ci gaba da harkokinsu kamar ba a yi tashin hankalin ‘yan bindiga ba.

Kar a manta duk lokacin da aka yi irin wannan taro gwamnatin Jihar Katsina na cewa babu hannunta kuma ba da ita aka yi sulhu ba, amma dai maganar jama’a na jin ta ne kamar abin nan ake cewa ihu bayan hari.

Karamar hukuma ta biyu da ita ma ta shiga sulhu da barayin daji ita ce, karamar hukumar Batsari, wanda ta sha fama da hare-haren ‘yan bindiga kamar ba gobe, an yi asarar rayuka da duniyoyi, amma yanzu sakamakon wannan zaman sulhu da aka shirya tsakanin al’ummomi da ‘yan bindigar abin ya yi sauki sosai.

Kwamishinan harkokin tsaro na cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa a kullum yana fada wa ‘yan jarida cewa babu ruwan gwamnatin Jihar Katsina da wancan sulhu, shi ne ya tabbatar da cewa idan aka je babbar asibitin Batsari za a ga ‘yan bindiga suna kwanshe suna karbar magani sakamakon cututtukan da suka dame su.

Ita ma karamar hukumar Danmusa ta sha fama da matsalar ‘yan bindiga sakamakon dukkan su suna makwabtaka da babban dajin Rugu da ke da iyaka da Jihar Zamfara, an yi dauki ba dadi a wannan karamar hukuma da barayin daji da al’umma da kuma jami’an tsaro.

Yanzu wadannan kananan hukumomi guda uku da aka ambata sun samu salama sun fara dawowa cikin hayyacin su, inda a yanzu kasuwanni suna cikar farin dango an fara tafiye-tafiye da daddare duk da cewa ana samun kai hare-hare jefi-jefi.

Wannan batun sulhu har gobe yana ci gaba da dore kan masana, musamman wadanda suke da ra’ayin cewa ka da a yi sulhu da barayin daji kuma suke goyon bayan matsayar gwamnatin Radda.

Babban abin da ke dore kan masana da sauran al’umma shi ne, irin yadda gwamnati ke tinkaho da zaman lafiyar da aka samu a wadannan kananan hukumomi duk da ta cewa ba ruwan ta da wannan sulhu, wani lokaci har ikirarin cewa duk wanda ya saba alkawarin da aka yi da shi ba za ta kyale shi ba.

Rahotanni sun bayyana cewa duk wuraren da aka shirya wannan zaman sulhu bana an yi noma sosai, daman barayin daji ne suka hana noman a wadannan yankuna.

Da yawa daga cikin manoma da ‘yan kasuwa da direbobin da aka tattauna da su sun bayyana cewa lallai zaman lafiya na dawowa sannu a hankali duk da cewa wani lokaci ana da fargabar dawowa wannan hare-hare.

Yanzu dai abubuwan da suka bayyana shi ne, sakamakon wannan yarjejeniya da aka kulla da al’ummomi da barayin daji ana samun saukin kai hare-haren ‘yan bindiga, sai dai ba wai an daina kai harin bane baki daya ba, ana samun rahotanni kai hare-haren ‘yan bindiga jefi-jefi.

Masana da masu sharhi kan harkokin tsaro na jin tsoron wannan sulhu da aka ce al’umma ce da kanta ta shirya ba hannun gwamanti a ciki, daga cikin abubuwan da masana ke fargaba shi ne, barayin daji suna rike da makamansu, kuma ba a bayyane cewa an ba su kudi ba, me zai faru idan suna bukatar kudaden kashewa idan bukata ta taso masu?

Abin jira a gani shi ne, yadda wannan yarjejeniya za ta ci gaba da haifar da da mai ido ko akasin haka. Allah ya kyauta.

Sulhu
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
Sulhu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • Sulaiman
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.