ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: Sama Da Mutum Miliyan Daya Suka Yi Gudun Hijira A Arewa Maso Yamma – IOM

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
IOM

Akalla mutum 1,087,875 ne suka rasa matsugunansu sakamakon yawaitar ayyukan ‘yan bindiga da masu satar shanu da kuma masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya.

Rikicin ya fi shafar mata da yara, kashi 54 mata da kashi 56 na yara sun yi gudun hijira a Jihar Katsina, kuma jimillar mutanen da lamarin ya shafa sun kai 223,473.

  • Bayanin Da Amurka Ta Yi Kan Kudurin MDD Yaudara Ce Da Ta YI Wa Al’umma

An bayyana hakan ne a taron kaddamar da shirin sasanta rikici da sulhu a yankin arewa maso yammacin Nijeriya a hukumance, wanda hukumar kula da shige da fice ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM) ta shirya a Babban Birnin Jihar Katsina a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Shugaban hukumar ta IOM, Laurent De Boeck, ya bayyana cewa arewa maso yamma na fama da rikice-rikice tun daga shekarar 2014, wanda ya kai ga gudanar da bincike a watan Oktoban 2022 don gano karuwar tashe-tashen hankula, wanda ya shafi kimanin mutum sama da miliyan daya, a cikin wannan adadi kashi 29 cikin 100 ‘yan asalin Jihar Katsina ne.

Ya kuma kara tabbatar da cewa IOM, cibiyar habaka dimokuradiyya tare da taimakon Kungiyar Tarayyar Turai sun hada kai da gwamnatin Jihar Katsina domin inganta tsarin shiri sulhunta al’umma a jihar, da nufin rage rikice-rikice da inganta shirin samar da zaman lafiya a cikin gida da rage radadin talauci da inganta albarkatun kasa na arewa maso yammacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Aikin wanda ya kai kimanin watanni 18, ya fara ne tun daga Janairu 2022 zuwa Yuli 2023, za a gudanar da shi a kananan hukumomi hudu da suka hada da Dandume, Danmusa, Batsari da Jibia a Jihar Katsina.

Shima da yake jawabi a madadin gwamnatin jihar, kwamishinan harkokin cikin gida da tsaro, Nasiru Muazu Danmusa, ya gode wa abokan hulda na kasa da kasa kan wannan gagarimin aikin. Ya ce jihar na bukatar karin tallafi domin yaki da rashin tsaro da ya addabi wasu sassan jihar.

IOM
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Next Post
Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
IOM

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
IOM

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.